ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Fitar Da Sakamakon Bincike Game Da Yadda Kanada Ke Nuna Wa Kayayyakinta Wariya

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Sin

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Bayan da ta shafe tsawon rabin shekara tana gudanar da bincike da tattaro shaidu, a jiya Jumma’a kasar Sin ta fitar da sakamakon binciken da ta yi, game da yadda kasar Kanada take nuna wa kayayyakinta wariya, sakamakon da ya nuna cewa, irin matakin da Kanada ta dauka a shekarar da ta gabata, wato kara sanya harajin kwastam kan wasu hajojin da ta shigar daga kasar Sin, ciki har da motoci masu aiki da lantarki, da karafa da kuma sanholo, salo ne na nuna wariya. Don haka, kasar Sin ta mayar da martani bisa doka, inda ta kara sanya harajin kwastam kan wasu hajojin Kanada, al’amarin da ya sa aka fitar da rahoton bincike kan kin yarda da salon wariya, wanda ya zama irinsa na farko a duk fadin duniya.

A watan Agustan shekarar da ta gabata ne, kasar Kanada ta sanar da kara sanya harajin kwastam da kaso dari bisa dari, kan motoci masu aiki da karfin lantarki kirar kasar Sin, wanda ya fara aiki daga watan Oktoban shekara ta 2024, tare da kara harajin kwastam na kaso 25 bisa dari kan hajojin karafa da sanholo da kasar Sin ta samar. Makasudin yin hakan shi ne, hada baki da kasar Amurka, wajen sanyawa motoci masu aiki da karfin lantarki da kayan karafa da sanholo kirar kasar Sin harajin kwastam. Manazarta sun yi nuni da cewa, hajojin kasar Sin ne kadai, ita Kanada ta kara wa harajin kwastam, kuma ba tare da gudanar da cikakken bincike ba. Kana, fitar da irin wannan sanarwa ba tare da wata ingantacciyar hujja ba, salon wariya ne da Kanada ta yi, wanda ya kawo illa ga tsarin cinikayya na kasa da kasa.

  • A Mai Da Duniya Ta Zama Ta Kasa Da Kasa
  • Manchester United Na Son Lashe Firimiya A Shekarar 2028

Rahotannin sun kuma ruwaito cewa, a matsayinta na gani-kashe-nin Amurka, gwamnatin kasar Kanada ta sha nuna adawa da kasar Sin. Amma ba ta samu abun da take so ba. Tun bayan da sabuwar gwamnatin Amurka ta fara aiki tsawon kwanaki 40 ko fiye, ya zuwa yanzu, sau da dama ta ci zarafin Kanada, inda ta ce Kanada “jiha ce ta 51 a Amurka”, har ma ta yi mata barazana ta hanyar sanya harajin kwastam. Irin wannan abun ya zama gargadi ga wasu kasashe ’yan kalilan, wadanda ke fatan samun “afuwa” daga Amurka, bisa matakin da suka dauka kan kasar Sin.

ADVERTISEMENT

Kasar Sin ba za ta rura wutar rikici ba, amma ba ta tsoro. Kuma tabbas za ta tsaya ga kiyaye muradun kasa da ikon samar da ci gaba, da kiyaye ka’idojin WTO game da tsarin cudanyar sassan kasa da kasa a fannin kasuwanci. (Murtala Zhang)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri
  • Sulaiman
    Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK
  • Sulaiman
    Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA
  • Sulaiman
    Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

MASU ALAKA

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA
Daga Birnin Sin

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026
Next Post
An Yi Cikakken Zama Na Uku Na Taron Shekara-Shekara Na Majalisar Bada Shawarwari Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin

An Yi Cikakken Zama Na Uku Na Taron Shekara-Shekara Na Majalisar Bada Shawarwari Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026
Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026
Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.