• English
  • Business News
Thursday, August 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muddin Nahiyar Afirka Ta Farka Ba Za A Iya Raina Ta Ba

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Muddin Nahiyar Afirka Ta Farka Ba Za A Iya Raina Ta Ba

A health worker administers a cervical cancer vaccine HPV Gardasil to a girl on the street in Ibadan, Nigeria, on May 27, 2024. African countries have some of the world's highest rates of cervical cancer. Growing efforts to vaccinate more young girls for the human papillomavirus are challenged by the kind of vaccine hesitancy seen for some other diseases. Misinformation can include mistaken rumors that girls won't be able to have children in the future. Some religious communities must be told that the vaccine is "not ungodly." More than half of Africa's 54 nations – 28 – have introduced the vaccine in their immunization programs, but only five have reached the 90% coverage that the continent hopes to achieve by 2030. (AP Photo/Sunday Alamba)

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan da kasar Amurka ta dakatar da bayar da tallafi ga kasashen Afirka, akwai mutanen da suka yi fushi, da wasu da suka fara daukar matakai, amma ba wanda ya yi rokon afuwa.

A kwanakin nan, kasar Amurka ta sanar da kawo karshen kaso 83% na ayyukan da ake tafiyar da su karkashin tsarin hukumar USAID, lamarin da ya haifar da tsaiko ga yarjeniyoyin hadin gwiwa 5200. Dangane da matakai masu alaka da batun, dan jarida a fannin kimiyya da fasaha Abdullahi Tsanni, ya rubuta a cikin wata mukalar da aka wallafa cikin mujallar Science da cewa, “Daukacin kasashen nahiyar Afirka sun yi fushi matuka”, saboda “an soke kudin tallafawa aikin hana yaduwar cututtuka, da yawansa ya kai biliyoyin daloli, da dakatar da gwaje-gwajen fasahohin jinya ba zato ba tsammani, lamarin da ya sanya mutane fiye da dubu dari 1 fuskantar yiwuwar rasa rayuka.”

  • Gwamna Buni Ya Naɗa Matasa 200 A Matsayin Hadimansa
  • Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutum 6 A Nasarawa

Sai dai bayan nuna takaici, ‘yan Afirka ba su daga tutar amana ko rokon afuwa ba. Maimakon haka, sun fara bincike a kai. Misali, Salim Karim, shugaban cibiyar nazarin cutar kanjamau ta kasar Afirka ta Kudu, ya ce janyewar tallafin Amurka wani gargadi ne ga kasashen Afirka, wanda ya nuna cewa “Kar a dogara da tallafin da sauran kasashen suke bayarwa wajen biyan bukatar kai, dole ne a yi kokarin dogaro da kai.”

A sa’i daya kuma, gwamnatocin kasashen Afirka sun fara daukar matakai. Inda a Najeriya, majalisar dattawa ta zartas da ware karin dalar Amurka miliyan dari 2 don tallafi a bangaren aikin jinya. Kana a kasashen Botswana, da Kamaru, da Kenya, hukumomi masu kula da aikin jinya sun yi alkawarin samar da kudin da ake bukata wajen kula da masu kamuwa da cutar kanjamau, yayin da gwamnatin kasar Afirka ta Kudu ta yi niyyar samar da kaso 83% na kudin da ake bukata a wannan bangare. Ko da yake akwai wuyar cike dukkan gibin da ke akwai ta fuskar kudin tafiyar da aikin jinya, amma dukkan kasashen Afirka sun nuna niyyar dogaro da kai. Hakan ya dace da maganar da shahararriyar masaniyar ilimin hana yaduwar cututtuka ta kasar Zimbabwe, Francisca Mutapi ta fada, wato “Kasashen yamma ba za su samar da dabarar daidaita matsalar aikin jinya a Afirka daga tushenta ba.”

Ma iya cewa karfin zuciya da kasashen Afirka suka nuna a wannan karo ya burge ni sosai, sai dai bai ba ni mamaki ba. Saboda na dade ina ganin alamar “farkar nahiyar Afirka”, da yadda kasashen Afirka suke daukar matakai bisa muradun kansu. Misali, bayan barkewar yaki tsakanin Ukraine da Rasha, kasashen Afirka sun ki daukar wani bangare tsakaninsu, ko da yake suna fuskantar matsin lamba daga kasashen yamma. Kana a fannin tattalin arziki, kasashen Afirka na kokarin gina wani babban yankin ciniki mai ‘yanci da ya shafi daukacin nahiyar Afirka. Yayin da a fannin tsaro, sun sa sojojin Faransa, da na Amurka janye jiki daga kasashen dake yammacin Afirka daya bayan daya.

Labarai Masu Nasaba

Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu

Hakika yadda kasar Amurka ta dakatar da tallafi a wannan karo ya nuna ra’ayin shugaba Donald Trump dangane da kasashen Afirka. Wanda za a iya fahimta bisa ganin yadda ya bayyana kasar Lesotho a matsayin “kasar da ba a san ta ba”, wacce ba ta cancanci tallafin da ake ba ta ba, a kwanakin baya, yayin da yake magana da ‘yan majalisun kasar Amurka. Sai dai shugaban bai san sauye-sauyen da kasashen Afirka suka samu ba, wadanda tun tuni suka daina dogaro da kasashen yammacin duniya.

A daura da haka, ana iya ganin fahimtar matsayin kasashen Afirka mai dacewa, a cikin maganar da ministan wajen kasar Sin Wang Yi ya fada a kwanan baya, yayin da yake amsa tambayar da wakiliyar kafar yada labaru ta Najeriya NAN ta gabatar masa. Inda ya bayyana nahiyar Afrika a matsayin wuri mai muhimmanci a karni na 21, wanda samun kwanciyar hankali da ci gaban tattalin arzikinsa ya shafi makomar bai daya ta daukacin dan Adam. Sa’an nan, bayan da ya yi bayani kan kokarin da kasar Sin ta yi wajen haifar da takamaiman ci gaba a kasashen Afirka, jami’in na Sin ya ce, “Nahiyar Afirka na cikin wani sabon mataki na farkawa. Kamata ya yi a mara musu baya, don su iya dogaro da kai wajen tafiya a kan sabuwar turbarsu ta raya kasa.” (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Buni Ya Naɗa Matasa 200 A Matsayin Hadimansa

Next Post

Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan’Adam 18 Daga Cibiyar Harba Kumbo Ta Kasuwanci Ta Hainan

Related

Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka
Ra'ayi Riga

Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

1 day ago
Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu
Ra'ayi Riga

Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu

5 days ago
Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?
Ra'ayi Riga

Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?

6 days ago
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe
Ra'ayi Riga

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

1 week ago
Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”
Ra'ayi Riga

Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”

2 weeks ago
Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna
Ra'ayi Riga

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

2 weeks ago
Next Post
Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan’Adam 18 Daga Cibiyar Harba Kumbo Ta Kasuwanci Ta Hainan

Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan’Adam 18 Daga Cibiyar Harba Kumbo Ta Kasuwanci Ta Hainan

LABARAI MASU NASABA

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

August 13, 2025
Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

August 13, 2025
APC

2027: Jagororin APC Na Kudu-maso-Yamma Sun Amince Da Tinubu Ya Sake Tsayawa Takara

August 13, 2025
Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

August 13, 2025
Tinubu

Rangwame: Tinubu Ya Bada Umarnin Sake Bitar Tsarin Yadda Ake Karɓar Haraji 

August 13, 2025
Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

August 13, 2025
Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

August 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

August 13, 2025
Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

August 13, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati

August 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.