• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kare-karen Harajin Amurka “Dara Ta Ci Gida”

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
Amurka

Yanzu haka dai Amurkawa sun fara girbar sakamakon matakan gwamnatin kasar mai ci na kara yawan harajin fiton kayayyaki da ake shigarwa kasar daga sassan duniya daban daban, inda matakin ya fara haifar da hauhawar farashi ga iyalai Amurkawa, wadanda suka fara tambayar halin da za su tsinki kai a ciki, idan har sauran sassan da Amurka ta kakabawa karin harajin suka fara aiwatar da nasu matakan na ramuwar gayya yadda ya kamata.

 

Rahotanni na cewa, tuni wasu Amurkawa suka fara gaggawar sayen kayayyakin bukatun yau da kullum, da nufin adanawa saboda tsaron abun da ka iya faruwa yayin da tasirin martanin kasashen duniya ya fara tsananta a kan kasarsu.

  • An Watsa Shirin Bidiyon “Bayanan Magabata Dake Jan Hankalin Xi Jinping” Na Harshen Cambodia
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 157, Sun Ƙwato Bindigu Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Tun farko dai masana sun sha bayyana wannan karin haraji na gwamnatin Amurka a matsayin matukar kwadayin cin kazamar riba, da yiwa saura matsin lamba domin cin gajiyar kashin kai bisa rashin adalci. Wannan mataki ya haifar da matsin lamba, da gurgunta managarcin tsarin gudanar da ayyukan masana’antu, da rarraba hajojinsu zuwa sassa daban daban na duniya. Baya ga hakan, matakin gwamnatin Amurkan zai jefa ci gaban tattalin arzikin duniya cikin wani mawuyacin yanayi, ciki har da na ita kanta Amurka.

 

LABARAI MASU NASABA

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Bugu da kari, illar matakin na Amurka na iya gurgunta salon hada-hadar kudade, da kwadago, da kirkire-kirkire da kasuwannin kasa da kasa ke cin gajiyarsu.

 

Bisa la’akari da tarihi, mun san cewa Sin da Amurka kasashe ne dake da banbance-banbance ta fuskar ci gaba, da yanayin gudanar masana’antu da karfin tafiyar da su, amma duk da haka ci gaban sassan biyu ya dunkule wuri guda, ta yadda illata sashe daya na iya haifar da koma baya ga dukkanin bangarorin biyu.

 

Ga misali, yayin da gwamnatin Amurka ke ta yayata manufar karin harajin ramuwar gayya, kamata ya yi mu lura cewa, Amurka na shigo da tarin hajoji da aka kammala sarrafawa, da wadanda ake kara sarrafawa a cikin kasar daga kasar Sin, matakin da ya yi matukar karfafa sashen masana’antun Amurka, ya kuma samarwa Amurkawa masu sayayya damar samun zabi na sayayya, da rahusar farashin abubuwan bukata na rayuwar yau da kullum, da karfafa ikon Amurkawa na sayen hajoji daban daban musamman ma masu matsakaici da karancin kudin shiga.

 

La’akari da hakan, za mu kara fahimtar cewa, ta hanyar hadin gwiwa tsakanin Sin da Amurka ne kadai manyan kamfanoni, da masana’antun Amurka za su iya kaiwa ga shiga a dama da su a fannin goyayya, da karfafa dunkulewar tattalin arzikinsu, sabanin yadda a yanzu Amurka ke yin matsin lamba, da kakaba haraji na cin zali, wanda zai gurgunta tattalin arzikin dukkanin sassa baki daya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka
Daga Birnin Sin

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
Next Post
Sojojin Nijeriya Sun Yi Lugudan Wuta Kan Sansanin Ƴan Ta’adda A Borno

Sojojin Nijeriya Sun Yi Lugudan Wuta Kan Sansanin Ƴan Ta'adda A Borno

LABARAI MASU NASABA

Maganin Nankarwa (4)

Maganin Nankarwa (4)

November 8, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Wata Budurwa Hukuncin Shekaru 4 A Kano, Duba Laifinta

Kotu Ta Yanke Wa Wata Budurwa Hukuncin Shekaru 4 A Kano, Duba Laifinta

November 8, 2025
NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

November 8, 2025
Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

November 8, 2025
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

November 8, 2025
Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

November 8, 2025
An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.