• English
  • Business News
Sunday, September 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hyda Ghaddar: Mai Son Horar Da ‘Yanmatan Kano Kwallon Kafa

by Abba Ibrahim Wada
5 months ago
in Wasanni
0
Hyda Ghaddar: Mai Son Horar Da ‘Yanmatan Kano Kwallon Kafa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai koyarwa Hyda Ahmad Ghaddar, mai shekaru 27 da haihuwa, tana horar da matasa kwallon kafa a kungiyarta mai suna ‘Breakthrough Football Academy’, ma’ana makarantar da matasa za su samu damar tsallakawa zuwa kasashen waje cikin sauki kuma ba tare da yaudara ba ko kuma damfara kamar yadda aka bayyana wasu makarantun suna yi wa matasan da suke son tsallakawa nahiyar turai.

Matashiya Hyda, ta fara buga kwallo ne tun tana ‘yar shekara shida da haihuwa tare da ‘yan uwanta a kofar gida a cikin birnin Kano.

  • Kwararru Sun Yi Musayar Ra’ayoyi Dangane Da Wayewar Kan Sin Da Afirka 
  • Yadda Hukuncin Kotun Koli Ya Kara Dagula Rikicin Shugabanci A PDP Da LP

An dai haifi Hyda a Lebanon amma iyayenta sun koma birnin Kano a lokacin da take ‘yar watanni biyu, inda ta shafe shekara 16 a Kano kafin daga baya ta sake komawa kasar Lebanon din bayan kammala karatun jami’a a Jihar Kano.

A kasar tata ta asali wato Lebanon ne Hyda ta tsunduma harkar wasan kwallon kafa gadan-gadan, inda har ta shiga makarantu na samun horo a fannin horar da kwallon kafa a Lebanon da Burtaniya. Sannan ta buga kwallon kafa a Nijeriya da Sifaniya da Burtaniya da kuma Lebanon, amma kuma Hyda ta so yin kwallo kafa a matsayin kwararriyar ‘yar kwallo sai dai a sakamakon rauni da ta samu ya sa sauya tunaninta zuwa mai horar da ‘yan kwallon kafa.

Ta yi digirinta na farko a fannin kimiyyar motsa jiki da kiwon lafiya wato PHE, sannan ta yi digiri na biyu sannan ta yi kwasa-kwasai a fannin kociya har ma ta yi karatun bayar da horo ga masu son zama kociya, sannan tana kuma da lasisi daban-daban kan horar da ‘yan kwallo wanda hakan ne ya kara mata kwarin gwiwa na ganin ta dage wajen cimma burinta na koyarwa.

Labarai Masu Nasaba

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo

Hyda ta bude kungiyar kwallon kafa ta ‘Breakthrough Football Academy’ a Kano watanni shida da suka gabata inda take da burin bai wa Kanawa dama su shiga duniyar wasanni inda a hirarta ta sashin Hausa na BBC ta ce ta zama kociya ce saboda tunanin da take da shi na taimakon al’ummar Kano bisa la’akari da irin taimakon da al’ummar Kano suka yi mata itama.

Ta ce “Babban burina shi ne samun wasu daga cikin wadanda nake bai wa horo sun yi fice a duniyar kwallo.” Ta kuma kara da cewa wani karin burin nata shi ne a samu babbar kungiyar wasa ta mata zalla a Kano “Domin a Kano akwai matan da suka iya kwallon kafa amma saboda rashin dama ba a jin su.”

Kungiyar tata mai suna ‘Breakthrough Football Academy’ na gayyato ‘yan wasa kuma “idan sun ga mutum ya yi musu sai su rike shi idan kuma bai dace ba sai su ba shi hakuri. Hyda Ahmad Ghaddar ta yi wasan kwallon kafa inda kuma ta fi taka ‘yar wasan tsakiya sannan ta ce ta samu kwarin gwiwa daga iyalinta tun daga farko kasancewarsu masu son kwallon kafa ne.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hydaa GaddarKwalloMataMatashiya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tawagar CPPCC Ta Ziyarci Nijeriya Da Cote d’Ivoire Da Senegal

Next Post

Ma’aikatar Kasuwancin Sin: Dole Ne Amurka Ta Daina Dora Laifi Kan Sauran Kasashe

Related

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda
Wasanni

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

19 hours ago
Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo
Wasanni

Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo

3 days ago
Lookman
Wasanni

Kofin Duniya: Lookman Da Dessers Sun Isa Sansanin Super Eagles A Uyo

4 days ago
Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG
Wasanni

Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

6 days ago
Isak Na Dab Da Zama Ɗan Wasa Mafi Tsada A Tarihin Firimiya
Wasanni

Isak Na Dab Da Zama Ɗan Wasa Mafi Tsada A Tarihin Firimiya

6 days ago
Yadda Kungiyoyin Firimiyar Ingila Suka Shirya Wa Kakar Bana
Wasanni

Yadda Kungiyoyin Firimiyar Ingila Suka Shirya Wa Kakar Bana

1 week ago
Next Post
Ma’aikatar Kasuwancin Sin: Dole Ne Amurka Ta Daina Dora Laifi Kan Sauran Kasashe

Ma’aikatar Kasuwancin Sin: Dole Ne Amurka Ta Daina Dora Laifi Kan Sauran Kasashe

LABARAI MASU NASABA

Shawara Ga Matashin Da Matarsa Ta Samu Juna Biyu (1)

Shawara Ga Matashin Da Matarsa Ta Samu Juna Biyu (1)

September 7, 2025
Hanyoyin Kare Kai Daga Cutar Basir Cikin Sauƙi

Hanyoyin Kare Kai Daga Cutar Basir Cikin Sauƙi

September 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

September 7, 2025
Arewa

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

September 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

Kwamishinan ‘Yansandan Abuja Ya Gargadi Jami’ansa Kan Arangama Da Direbobi A Titi

September 7, 2025
Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

September 7, 2025
ASUU

Malaman Jami’o’i Sun Zama Abin Tausayi —Kungiyar ASUU

September 7, 2025
Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya

Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya

September 7, 2025
Zulum Ya Tabbatar Da Harin Boko Haram Ya Ci Rayukan Mutane 63 

Zulum Ya Tabbatar Da Harin Boko Haram Ya Ci Rayukan Mutane 63 

September 7, 2025
Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.