ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar Shari’a Ta Dakatar Da Magatakarda 2, Ta Kuma Gargaɗi Alƙalai 2 A Kano

by Sulaiman
8 months ago
kotu

Hukumar kula da shari’a ta jihar Kano ta dauki matakin ladabtarwa a kan wasu jami’an kotuna hudu, inda ta dakatar da wasu magatakarda biyu tare da yin gargadi ga alkalan kotun shari’a biyu bisa nuna rashin kwarewa da cin zarafin aikinsu.

 

Mai magana da yawun hukumar, Baba Ibrahim ne ya fitar da sanarwar daukar hukuncin ladabtarwar.

ADVERTISEMENT
  • Ƴansanda Sun Damke Ango Da Abokansa Bayan Mutuwar Amarya A Jigawa
  • Liverpool Sun Zama Zakaran Gasar Premier Bayan Lallasa Tottenham

Ibrahim ya bayyana cewa, an cimma matsayar ne a yayin taron hukumar karo na 80 da aka gudanar a ranar 22 ga Afrilu, 2025, bisa ga shawarwarin kwamitin korafe-korafen jama’a na bangaren shari’a.

 

LABARAI MASU NASABA

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Daga cikin wadanda aka dakatar har da Ibrahim Adamu, babban magatakarda na biyu a babbar kotun shari’a, wanda aka dakatar da shi ba tare da biyansa albashi ba na tsawon watanni shida.

 

Har ila yau, an dage kara masa girma bayan da aka same shi da laifin zagi da kuma yunkurin kai wa nagaba da shi hari – wanda ya saba wa dokokin ma’aikatan jihar Kano (2004) da kuma dokokin hukumar kula da harkokin shari’a.

 

A wata shari’ar kuma, Maigida Lawan, babban magatakarda na kotun daukaka kara ta Shari’a, an hukunta shi ne bisa laifin nema tare da kuma yunkurin biyan bukatun kansa ta hanyar da bata dace ba – karya.

 

Hukumar ta rage masa girma daga mataki na 13 zuwa mataki na 12 sannan ta dakatar da shi ba tare da biyansa albashi ba na tsawon watanni shida, nan take.

 

Har ila yau, Alkalin Kotun Shari’ar Musulunci, Alkali Mansur Ibrahim, ya samu gargadi a hukumance bayan da aka tabbatar da cewa ya yi kalaman batanci ga mai kara.

 

An kuma gargadi abokin aikin sa Alkali Nasiru Ahmad, biyo bayan nuna bangaranci a shari’ar da ya yi.

 

Hukumar ta sake jaddada matsayar ta na yaki da cin hanci da rashawa da rashin da’a, inda ta yi gargadin cewa, duk wani jami’in kotu da aka samu da aikata rashin da’a zai fuskanci hukuncin ritayar dole.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani
Manyan Labarai

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Next Post
Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara

Cibiyar Yaƙi da Ta'addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da 'Yan Bindiga A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.