• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Rububin Sayen Kuri’u A Tsakanin ‘Yan Siyasa – Kwamishinan Zabe

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
sayen kuri'u
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamishinan hukumar zaben Jihar Ribas, Obo Effanga ya bayyana cewa babban abin da ke rusa ci gaban kasar nan shi ne, yadda mafi yawancin ‘yan siyasan Nijeriya suke sayan kuri’u.

Ya ce hukumar zabe tana gudanar da wasu shirye-shirye masu karfi da zai tabbar dakile wannan mummunar dabi’a.

  • Hadin Gwiwar Afirka Da Sin Na Taimakawa Raya Duniya

A kwanan nan ne hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) tana nada Effanga a matsayin kwamishinan zaben Jihar Ribas. Ya bayyana hakan ne a lokacin wata liyafa da ta gudana a Abuja.

Ya ce, “A yanzu yadda ‘yan siyasa ke sayan kuri’u ya nuna cewa wadannan kuri’u suna da matukar muhimmanci kuma dole da su ne za su iya samun nasara a zabe. Saboda a yanzu ana kirga kuri’un mutane shi ya sa ‘yan siyasa suke bin duk wata hanya da za su sayi kuri’u,” in ji Effanga.

Ya kara da cewa ‘yan siyasa sun gano cewa watakila wannan ce hanya mafi saukin samun nasara shi ya sa suke bai wa mutane kudi domin su saye kuri’unsu.
Ya ce a bangaren INEC, duk mutumin da ya cancanci jefa kuri’a za a bar shi ya yi zabe. A cewarsa, lokacin da mutum ya yi zabe za a kirga kuri’arsa sa’ilin da aka kammala zabe.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

Ya ci gaba da cewa dabi’ar sayan kuri’a tana matukar kawo matsala ga ci gaban kasa.
Kwamishinan zabe ya ce duk dan Nijeriya da yake da sha’awar samun dimokuradiyya mai inganci, ya tabbatar da cewa bai sayar da kuri’arsa ba. Ya ce hakan zai iya faruwa ne a lokacin da aka fadakar da ‘yan Nijeriya illar sayar da kuri’arsu.

Effanga ya ce gudanar da zabe a kan tsari shi ke karfafa dimokuradiyya, wannan shi ya sa manyan mutane a Nijeriya suka tashi tsaye na ganin cewa hukumar zabe ba ta samu cin gashin kanta ba, wannan ne ya sa mafi yawancin zaben kananan hukumomi ake tafka magudi na ganin sai jam’iyya mai mulki ta samu nasara.

Kwamishinan zabe ya bayyana cewa yin rajistar zabe fiye da daya ya janyo mafi yawancin mutane ba za su samu nasarar jefa kuri’a ba. Ya ce an dakatar da katin zabe na mafi yawancin mutane saboda sun yi rajista fiye da guda daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Buhari Ya Rantsar Da Dakta Bello A Matsayin Shugaban Hukumar Raba Dai-Dai

Next Post

Yadda ‘Hackers’ Ke Amfani Da Smishing Wajen Yin Kutse

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

1 week ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

1 week ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

1 week ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

2 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

2 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

2 weeks ago
Next Post
Yadda ‘Hackers’ Ke Amfani Da Smishing Wajen Yin Kutse

Yadda 'Hackers' Ke Amfani Da Smishing Wajen Yin Kutse

LABARAI MASU NASABA

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

September 14, 2025
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

September 14, 2025
Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

September 14, 2025
Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

September 14, 2025
Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

September 14, 2025
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

September 14, 2025
Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

September 14, 2025
An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025

An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025

September 14, 2025
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

September 14, 2025
Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.