• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dattawa Ta Kafa Kwamitin Sa Ido Kan Gwamnatin Riƙo A Ribas

by Sadiq
6 months ago
Ribas

Majalisar Dattawa ta kafa wani kwamiti mai mutum 18 domin sa ido da bin diddigin yadda gwamnan riƙo na Jihar Ribas, Vice Admiral Ibok Ete Ibas (mai ritaya), ke gudanar da mulki tun bayan ayyanar dokar ta-ɓaci a jihar.

Shugaban. Majalisar, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana hakan yayin zaman majalisar na ranar Talata, inda ya ce kafa kwamitin zai taimaka wajen tabbatar da shugabanci na gaskiya da kuma ganin an bi doka yadda ya kamata a jihar.

  • EFCC Ta Kama Matashi A Kaduna Bisa Zargin Wulaƙanta Naira A Bidiyon Barkwanci
  • Za A Gudanar Da Taron Tallata Fim Din “Red Silk” A Moscow

Ya ce, “Wannan mataki wani ɓangare ne na ƙoƙarin tabbatar da zaman lafiya da bin doka a Jihar Ribas, ba tare da wata ɓoyayyar manufa ba.”

Kwamitin, wanda shugaban masu rinjaye, Sanata Opeyemi Bamidele ke jagoranta, ya ƙunshi Sanata Adamu Aliero, Osita Izunaso, Osita Ngwu, Kaka Shehu, Aminu Abass, Tokunbo Abiru, da Adeniyi Adebire, tare da wasu ƙarin mambobi.

Tun a watan Maris ne shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ya ayyana dokar ta-ɓaci a Jihar Ribas saboda rikicin siyasa da ya ɓarke tsakanin gwamnan jihar, Siminalayi Fubara na jam’iyyar PDP, da tsohon gwamnan jihar, Nyesom Wike, wanda yanzu ke cikin gwamnati a matakin tarayya a matsayin minista.

LABARAI MASU NASABA

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

Rikicin ya janyo zaman ɗari-ɗari a jihar, lamarin da ya sa shugaban ƙasa ya tsoma baki domin kare zaman lafiya da doka a jihar.

Gwamnan riƙo Ibok Ete Ibas ne aka ɗora don tafiyar da mulki har sai an samu daidaito a siyasar jihar.

Ana sa ran kwamitin za ta kai rahoto a duk matakin da take gani ya kamata a ɗauka domin kare mulkin dimokuraɗiyya da kwanciyar hankali a Jihar Ribas, wadda ke daga cikin muhimman jahohin da ke da tasiri a tattalin arziƙin Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP
Labarai

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!
Rahotonni

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato
Labarai

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

November 7, 2025
Next Post
Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan Hulɗa

Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan Hulɗa

LABARAI MASU NASABA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

November 7, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

November 7, 2025
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

November 7, 2025
Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.