• English
  • Business News
Monday, October 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Kin Amincewar Kwankwaso Zuwa APC: Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Mai Taimaka Ma Ta

by Sulaiman
5 months ago
Kano

Gwamnatin jihar Kano ta dakatar da wani mai taimaka ma ta kan harkokin siyasa, Ibrahim Rabi’u, sakamakon fitar da wata sanarwa ta karya mai cike da cece-ku-ce da ake dangantawa da Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, shugaban jam’iyyar NNPP kan cewa, ya ki amincewa da tayin da shugaba Bola Tinubu ya yi masa na komawa jam’iyyar APC.

 

Sanarwar dakatarwar wacce ta fara aiki a ranar Asabar, 17 ga Mayu, 2025, ta fito ne a cikin wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar, Umar Farouk Ibrahim, sannan mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya bayyana.

  • Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure
  • Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

A cewar sanarwar, Rabi’u, wanda ke aiki a matsayin babban mai ba da rahoto na musamman (SSR) a ma’aikatar sufuri, an dakatar da shi ne saboda “furucin da ya yi da sunan Kwankwaso kuma ba tare da izininsa ba”.

 

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

Gwamnati dai ta nisanta kanta daga labarin na karya, inda ta kwatanta batun da cewa, “mai tada hankali da rashin izini”.

 

Gwamnatin jihar ta kuma gargadi dukkan masu rike da mukaman siyasa da su daina bayyana ra’ayoyinsu da sunan Gwamnati kan wasu muhimman batutuwan da suka shafi siyasa ba tare da tantancewa ba.

 

LEADERSHIP ta fahimto cewa, wannan matakin ya biyo bayan wani labari ne da aka yada da cewa, Sanata Kwankwaso ya ki amincewa da tayin da shugaba Tinubu ya yi masa na tsunduma shi cikin jam’iyyar APC, inda ake zargin Sanatan ya bayyana cewa, ya gwammace ya bar siyasa maimakon ya koma jam’iyya mai mulki.

 

Ba da dadewa ba, wannan labarin na karya ya samu karbuwa a shafukan sada zumunta wanda Kwankwaso da gwamnatin Kano, tuni suka yi martani a kai.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina
Labarai

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

October 27, 2025
Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

October 27, 2025
Next Post
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (I)

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (I)

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

October 27, 2025
Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

October 27, 2025
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Ba Za A Samu Ƙarancin Man Fetur A Lokutan Bukukuwan Ƙarshen Shekara Ba – Dangote 

October 27, 2025
An Zaɓi Birgediya Janar Yake A Matsayin Sarkin Sayawa Na Farko Duk Da Zanga-zanga 

An Zaɓi Birgediya Janar Yake A Matsayin Sarkin Sayawa Na Farko Duk Da Zanga-zanga 

October 27, 2025
Kwankwaso

Tsohon Gwamnan Jigawa, Lamido Ya Bayyana Aniyar Takarar Shugabancin Jam’iyyar PDP Na Ƙasa

October 27, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno

October 27, 2025
Hatsarin Jiragen Ruwa

Matasa 5 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Gombe

October 27, 2025
Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

October 26, 2025
Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

October 26, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.