Manchester City ta amince da yarjejeniya tare da AC Milan kan daukar dan wasan tsakiya na Holland Tijjani Reijnders, wannan cinikin zai kasance na farko da City za ta yi idan aka bude kasuwar saye da sayar da ‘yan kwallo ta bazara, in ji rahotanni.
Zakarun gasar Firimiya na shekarar 2024 Manchester City na shirin biyan Yuro miliyan 55 kwatankwacin Dalar Amurka miliyan 63 domin daukar dan wasan mai shekaru 26, wanda aka fahimci ya amince da kwantiragin shekaru biyar a Etihad, City na fatan kammala cinikin dan wasan na Netherlands kafin lokacin gasar cin kofin duniya ta kungiyoyin kwallon kafa na FIFA da za a fara a ranar 14 ga watan Yuni.
- Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027
- Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba
Reijnders ya koma AC Milan ne daga AZ Alkmaar a shekara ta 2023 kuma ya ci wa kungiyar ta Italiya kwallaye 15 a kakar wasanni ta shekarar 2024/2025, zuwan Rijnders zai kara yawan zabukan da Pep Guardiola ke da shi a tsakiya bayan tafiyar Kebin De Bruyne, ba a tsammanin tsohon dan wasan na Belgium zai taka leda a gasar cin kofin duniya, inda ake ganin zai iya komawa Napoli mai rike da kofin Seria A.
Mateo Kobacic ba zai samu damar buga gasar cin kofin Duniya na kungiyoyi ba sakamakon tiyatar da aka yi masa a Achilles (Gwuiwa), kungiyar da Pep Guardiola ke jagoranta ta sha fama da rashin nasara a kakar wasa ta 2024/25, inda ta kare a matsayi na uku a gasar Firimiya kuma ta kasa lashe kofi a karon farko cikin shekaru takwas.
A makon da ya gabata shugaban City Khaldoon Al Mubarak ya yarda cewa kulob din ya kamata ya kashe kudade masu yawa a kasuwar musayar yan wasa gabanin fara kakar wasa ta badi domin karfafa kungiyar, City za su je gasar cin kofin duniya na kungiyoyi 32 da aka fadada a matsayin masu rike da kofin gasar bayan sun lashe gasar da aka yi a Saudiyya shekaru biyu da suka wuce.
Za su fara wasansu na farko da kungiyar Wydad Casablanca ta Morocco a Philadelphia ranar 18 ga watan Yuni, za a bude kasuwar musayar ‘yan wasa har zuwa ranar 10 ga watan Yuni domin karbar kungiyoyin da ke son sayen ‘yan wasa a gasar cin kofin duniya kafin a sake budewa a ranar 16 ga watan Yuni.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp