• English
  • Business News
Thursday, June 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƙungiyar G-5 Ta Ceto Nijeriya Daga Faɗa Wa Rikici — Wike

by Sadiq
2 days ago
in Manyan Labarai
0
Ƙungiyar G-5 Ta Ceto Nijeriya Daga Faɗa Wa Rikici — Wike
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya ce ƙungiyar G-5 ta taimaka wajen hana aukuwar rikici a Nijeriya. 

Ya bayyana haka ne a wani taro da ya yi da shugabannin jam’iyyar PDP a Abuja.

  • Sojoji Sun Kashe Manyan ‘Yan Boko Haram A Gujba Da Malamfatori
  • Bam Ya Hallaka Masu Yawon Sallah A Sakkwato

Wike, wanda yana daga cikin manyan membobin G-5, ya ce ƙungiyar ta yi adawa da rashin adalci a PDP kafin zaɓen 2023.

Ya ce da jam’iyyar ta saurari kiransu na sauya mulki zuwa Kudu bayan shekaru takwas na Shugaba Buhari, ba za ta fuskanci matsalar ba.

“Kuna iya tsanarmu, amma gaskiya ce, ayyukanmu sun ceto Nijeriya,” in ji Wike.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara

Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane

“Mun bi tsarin mulki kuma mun ƙi rashin adalci. Da PDP ta yi haka, ba za ta fuskanci wannan matsala ba.”

Taron ya haɗa da tsoffin gwamnonin jihohi Samuel Ortom (Benue) da Okezie Ikpeazu (Abia), da sauran shugabannin jam’iyyar.

Wike ya soki shugabannin PDP saboda sanya son rai fiye da haɗin kan jam’iyyar.

Ya ce jam’iyyar sai ta koma tubalinta na asali don samun ci gaba.

“Wasu shugabanni suna karkatar da dokoki don amfanin kansu,” in ji Wike, yana ambaton yadda gwamnan Taraba ya tsaya takarar gwamna ba tare da ya yi murabus a matsayinsa na shugaban jam’iyyar ba.

“Dole ne a daina wannan.”

Tsohon Gwamna Ortom ya yarda da maganar Wike, ya amince cewa PDP ta yi manyan kurakurai.

“Muna buƙatar taimakon Allah don gyara jam’iyyar,” in ji shi.

Ƙungiyar G-5 wadda ta haɗa da Wike, Ortom, Ikpeazu, Ifeanyi Ugwuanyi (Enugu), da Seyi Makinde (Oyo), sun yi adawa da takarar Atiku Abubakar a zaɓen 2023, wanda suka ce hakan ya saɓa wa dokar tsarin karba-karba.

Adawar ta jefa jam’iyyar PDP cikin matsalolin wanda hakan ya kai ta ga faɗuwa zaɓen 2023.

Yanzu, Wike yana aiki a ƙarƙashin Shugaba Tinubu amma har yanzu yana iƙirarin shi memba ne na jam’iyyar PDP, wanda ke ƙara dagula wa jam’iyyar lissafi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: G-5PDPWike
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojoji Sun Kashe Manyan ‘Yan Boko Haram A Gujba Da Malamfatori

Next Post

Trump: Yadda Sabuwar Dokar Hana Shiga Amurka Ta Fi Shafar Musulmai Da Afirka

Related

Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara

2 hours ago
Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane
Manyan Labarai

Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane

5 hours ago
EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Zargi Aikata Damfara A Intanet A Kaduna
Manyan Labarai

EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Zargi Aikata Damfara A Intanet A Kaduna

6 hours ago
Zan Ci Gaba Da Ɓata Wa Masu Sukar Tinubu Rai Da Ayyuka – Wike
Manyan Labarai

Zan Ci Gaba Da Ɓata Wa Masu Sukar Tinubu Rai Da Ayyuka – Wike

10 hours ago
Duk Da Cewa Wike Ba Ɗan APC Ba Ne Amma Muna Jin Daɗin Aikin sa – Tinubu
Manyan Labarai

Duk Da Cewa Wike Ba Ɗan APC Ba Ne Amma Muna Jin Daɗin Aikin sa – Tinubu

23 hours ago
Irin Ministocin Da ‘Yan Nijeriya Ke Tsammani Daga Gwamnatin Tinubu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Soke Faretin Ranar Dimokuraɗiyya, Tinubu Zai Yi Wa ‘Yan Ƙasa Jawabi 

1 day ago
Next Post
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump: Yadda Sabuwar Dokar Hana Shiga Amurka Ta Fi Shafar Musulmai Da Afirka

LABARAI MASU NASABA

An Bude Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afirka A Changsha

An Bude Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afirka A Changsha

June 12, 2025
Aliko Dangote Ya Sauka Daga Shugabancin Kamfanin Sukarin Dangote

Aliko Dangote Ya Sauka Daga Shugabancin Kamfanin Sukarin Dangote

June 12, 2025
Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara

Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara

June 12, 2025
Ya Kamata Ana Kammala Shari’ar Zaɓe Kafin Rantsuwa

Ya Kamata Ana Kammala Shari’ar Zaɓe Kafin Rantsuwa

June 12, 2025
Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane

Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane

June 12, 2025
Kocin Kano Pillars Usman Abdullahi Ya Ajiye Aikinsa

Kocin Kano Pillars Usman Abdullahi Ya Ajiye Aikinsa

June 12, 2025
EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Zargi Aikata Damfara A Intanet A Kaduna

EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Zargi Aikata Damfara A Intanet A Kaduna

June 12, 2025
Basaraken Da Aka Sace A Kogi Ya Kuɓuta Bayan Shafe Kwanaki 27 A Hannun ‘Yan Bindiga 

Basaraken Da Aka Sace A Kogi Ya Kuɓuta Bayan Shafe Kwanaki 27 A Hannun ‘Yan Bindiga 

June 12, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Gidan Mai A Legas

Gobara Ta Ƙone Wani Gidan Mai A Legas

June 12, 2025
Zan Ci Gaba Da Ɓata Wa Masu Sukar Tinubu Rai Da Ayyuka – Wike

Zan Ci Gaba Da Ɓata Wa Masu Sukar Tinubu Rai Da Ayyuka – Wike

June 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.