• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A gun taron ministoci game da tantance ayyukan aiwatar da sakamakon da aka samu a dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka, da ya gudana a birnin Changsha na Sin a kwanan nan, kasar Sin ta sanar da cewa, za ta yafe harajin fito kan dukkan kayayyakin kasashe 53 dake nahiyar Afirka da ta kulla huldar diplomasiyya da su. Hakan ya nuna cewa, kasar Sin tana kokarin cika alkawarin da ta yi na gina “al’ummar Sin da Afirka mai kyakkyawar makomar bai daya”.

Ban da kasashe 33 masu karancin tattalin arziki dake nahiyar Afirka, da tuni suka ci gajiyar manufar Sin ta yafe harajin kwastam, sabbin kasashe 20 dake Afirka da za su ci gajiyar manufar, sun hada da Najeriya, da Masar, da Afirka ta Kudu, da kuma Aljeriya, wato kasashe hudu mafi karfin tattalin arziki a Afirka. Wadannan kasashe, a bisa tushen karfinsu a fannin tattalin arziki, za su iya amfani da manufar kasar Sin wajen kara habaka bangaren fitar da kayayyaki zuwa kasuwannin Sin sosai. Bugu da kari, game da wasu kasashen Afirka da ke da gibin ciniki da kasar Sin, manufar yafe haraji ta kasar za ta taimaka wajen daidaita cinikayyarsu da kasar Sin.

  • Tinubu Ya Kai Ziyara Benuwe Sakamakon Kisan Kiyashi Da Aka Yi Wa Jama’a
  • An Ɗaure Wani Mutum Wata 6 Kan Satar Takalma A Masallaci A Kaduna

Idan aka waiwayi yadda aka raya dangantakar tattalin arziki da ciniki tsakanin Sin da Afirka cikin shekaru 20 da suka gabata, za mu iya ganin cewa, manufar rangwame a fannin harajin kwastam da kasar Sin ta samar wa kasashen Afirka ta yi ta fadada zuwa fannoni daban daban.

Tun a shekarar 2005, kasar Sin ta fara daukar matakan rage harajin fito kan kayayyakin kasashen Afirka da ke da raunin tattalin arziki, kuma ya zuwa shekarar 2010, manufar ta shafi kashi 60 cikin 100 na kayayyakin kasashe 26 dake nahiyar Afirka. Sa’an nan, daga shekarar 2022, kasar Sin sannu a hankali ta fara aiwatar da matakin yafe haraji kan kaso 98% na kayayyakin kasashe 27 dake Afirka. Bayan haka, a gun taron kolin dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka na shekarar 2024 da aka gudanar a birnin Beijing, shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya sanar da yafe harajin kwastam kan dukkan kayayyakin da ake shigowa kasar Sin daga kasashen Afirka 33 da suka fi fama da koma bayan tattalin arziki wadanda suka kulla huldar diplomasiyya tare da ita. Sai kuma ga shi a yanzu, manufar yafe haraji ta kasar Sin ta shafi dukkan kasashe 53 dake nahiyar Afirka, da suka kulla huldar diplomasiyya tare da ita.

Ba kamar wasu matakan ciniki da suka jibanci Afirka, da kasashen yamma suka gabatar a baya ba, wadanda ke shafar manufofin siyasa da yunkurin gyaran tsare-tsaren Afirka, manufofin kasar Sin suna da halayen musamman guda uku: Wato da farko, ba a taba gindaya sharadi na siyasa ba. Kana na biyu, manufofin suna dorewa. Gami da na uku, wato kasar na tare da burin tabbatar da ci gaban tattalin arzikin Afirka.

Labarai Masu Nasaba

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ta hanyar inganta manufar yafe harajin kwastam a kai a kai, kasar Sin ta samar da yanayin kasuwanci mai karko a kasashen Afirka. Bugu da kari, kasar Sin tana kallon manufofinta na rangwame a matsayin matakan tabbatar da burin samun ci gaba, inda take kokarin kyautata tsarin cinikayyar waje na kasashen Afirka, da kuma ba da goyon baya wajen raya masana’antu, da habaka tsare-tsaren tattalin arziki a Afirka.

Dalilin da ya sa kasar Sin ke kokarin tabbatar da ci gabanta da kasashen Afirka na bai daya, shi ne domin ra’ayinta game da dangantakar dake tsakaninta da Afirka, wato al’ummar Sin da Afirka suna da makomar bai daya a nan gaba. A ganin kasar Sin, ita da Afirka suna da tarihi masu kama da juna, da kuma bukatun bai daya na raya kasa. Sa’an nan, a zamanin da muke ciki, yayin da ake fuskantar sauye-sauye a fannonin siyasa, da tattalin arziki, da kimiyya da fasaha, kasashe masu tasowa na cikin wani yanayi mai wuya ta fuskar raya tattalin arzikinsu. Saboda haka, Sin da Afirka ba za su iya cimma burinsu na samun ci gaban bai daya ba, sai dai ta hanyar hadin gwiwa da juna, a bangarorin tabbatar da adalci da gaskiya a duniya , da bude kofa, da tabbatar da moriyar kowa, da kyautata muhalli, da kuma kiyaye zaman lafiya. Bisa kokarin da ake na sauya nagartaccen tunani zuwa hakikanan matakai, ko shakka babu za mu shaida karin nasarorin da Sin da Afirka za su samu, a kokarinsu na zamanantar da al’ummunsu tare. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Kai Ziyara Benuwe Sakamakon Kisan Kiyashi Da Aka Yi Wa Jama’a

Next Post

Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne – Obasanjo

Related

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka
Ra'ayi Riga

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

19 hours ago
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya
Ra'ayi Riga

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

2 days ago
Tunawa Da Tarihi Tana Da Ma’anar Musamman
Ra'ayi Riga

Tunawa Da Tarihi Tana Da Ma’anar Musamman

1 week ago
Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka
Ra'ayi Riga

Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

2 weeks ago
Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu
Ra'ayi Riga

Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu

3 weeks ago
Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?
Ra'ayi Riga

Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?

3 weeks ago
Next Post
Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne – Obasanjo

Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne - Obasanjo

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hukumar NRC Ta Dakatar Da Zirga-zirgar Jiragen Kasa Na Abuja zuwa Kaduna

August 26, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

August 26, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

August 26, 2025
Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

August 26, 2025
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.