Sanata mai wakiltar Bayelsa ta Yamma, Seriake Dickson, ya bayyana cewa Shugaba Bola Tinubu, ya fi mayar da hankali kan harkokin siyasa da shirye-shiryen zabɓen 2027 fiye da gudanar da mulki, inda ya ke watsi da aiwatar da kasafin kuɗin ƙasar nan don ci gaban ƙasa.
Dickson ya bayyana hakan ne yayin muhawarar kan wani ƙudiri da Sanata Solomon Adeola, mai wakiltar Ogun ta Yamma, Shugaban Kwamitin Kasafi na Majalisar Dattawa, ya gabatar don tsawaita wa’adin aiwatar da kasafin shekarar 2024 zuwa ƙarshen Disambar 2025.
- Hatsarin Kwale-kwale: Rundunar Sojin Ruwan Nijeriya Ta Ceto Jami’an ‘Yansanda 8 Da Wani A Bayelsa
- Kotu Ta Daure Uban Da Ya Dirka Wa ‘Yarsa Ciki A Bayelsa
A cewarsa, har yanzu ‘yan Nijeriya ba su amfana da ɓangaren ci gaba na kasafin 2024 da Majalisar ta amince da shi ba, duk da cewa an riga an fitar da kuɗaɗen da suka shafi gudanarwa da albashi wanda ke cikin kasafin na yau da kullum, amma ba a aiwatar da na ɓangaren ayyukan ci gaba da jin dadin jama’a ba.
Sanatan ya bayar da misali da rahotannin da ke nuna cewa wasu ‘yan kwangila da suka kammala ayyukan gwamnati na ci gaba suna zanga-zanga saboda rashin biyan su hakkokinsu.
Ya kuma nuna damuwa cewa gwamnatin na kau da kai daga nauyin da ke kanta saboda siyasa, musamman shirye-shiryen zaɓen 2027 da kuma yawaitar masu sauya sheka zuwa jam’iyyar APC mai mulki, inda ya yi gargaɗi cewa ɓangarorin zartarwa da na dokoki na barin nauyin da kundin tsarin mulki ya dora musu.
Dickson ya goyi bayan buƙatar gudanar da bincike kan jinkirin aiwatar da kasafin yana mai jaddada cewa matsalar ba ta shafi rashin kudi ba tare da kira ga majalisar ta umarci kwamitocin kasafin kudi su gudanar da bincike cikin mako guda su kuma kawo rahoto.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp