• English
  • Business News
Thursday, May 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Girmama Cikakken ’Yanci Da Yankunan Kasa, Wajibi Ne A Kan Kowacce Kasa Babba, Ko Karama

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Girmama Cikakken ’Yanci Da Yankunan Kasa, Wajibi Ne A Kan Kowacce Kasa Babba, Ko Karama
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A matsayinta na shugabar kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya a wannan wata, kasar Sin, bisa jagorancin wakilinta na dindindin, ta kira taro kan samar da tsarin tsaro da ya dace da yanayin da ake ciki da girmama cikakken ’yanci da yankunan dukkan kasashe, domin samun yanayin tsaro mai karko a duniya. 

Hakika kiran wannan taron da Wakilin Sin Zhang Jun ya yi ta zo a daidai lokacin da ya dace, ganin yanayin kalubale da duniya take ciki da kuma yadda ake keta cikakken ’yancin kasashe da takalar fada da kuma ingiza tayar da rikici.

  • Sin Ta Bayyana Kalaman Jakadan Amurka A Sin A Matsayin Shaidar Dake Nuna Tunani Irin Na Danniya

Zamanin mulkin mallaka da danniya ko cinikin bayi ya wuce. Ana cikin wani sabon zamani da ake neman ci gaba ta hanyar girmamawa da moriyar juna.

Akwai bukatar kasashen da suke ganin su shafaffu da mai ne, su dai na kokarin dawo da hannun agogo baya, domin duniya ta ci gaba. Girmama cikakken ’yancin kasa ya zama wajibi a kan kowacce kasa babba, ko karama.

Kasashen duniya da al’ummominsu sun bambanta, suka san yanayin da suke ciki da manufofi mafi dacewa da su, kuma su kadai ne za su san yadda ya kamata su shawo kan matsalolin dake addabarsu.

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Har Da Na Amurka 

Hadin Gwiwar Sin Da Yankin Turai Na Kara Kawo Haske Ga Tattalin Arzikin Duniya

Don haka, bai kamata a rika nunawa kasashe fin karfi kan harkokinsu na gida ba, ko kuma a rika nuna musu an fi su sanin abun da ya fi dacewa da su ba.

Kamar yadda Zhang Jun ya bayyana yayin taron, dole ne a samu bambancin ra’ayi daga kasa da kasa kan batutuwan tsaro, amma ya kamata a samu daidaito ta hanyar tattaunawa da hadin gwiwa.

Shirin tsaron duniya da shugaban kasar Sin ya gabatar ga taron BOAO a watan Afrilu, ya gabatar da wata alkibla ta cimma tsaro na bai daya tare da warware matsaloli masu masu ruwa da tsaki.

An riga an san kasar Sin ba mai kaunar rikici ba ce, domin an ji, kuma an ga yadda al’ummominta da suka kunshi kabilu daban daban ke rayuwa cikin jituwa da zaman lafiya, don haka duk wani shiri da za ta gabatar don gane da hakan, a ganina abu ne da ya kamata a karba da hannu bibbiyu, tun da burinta shi ne, gina duniya mai kyakkaywar makoma cike da tsaro da kwanciyar hankali.

Akwai bukatar sauran kasashen duniya su mara mata baya, kuma su ma su yunkura, su hada karfi da karfi wajen ganin an samu ci gaban duniya da kwanciyar hankali, ta hanyar hakuri da girmama juna da tabbatar da adalci. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kyan Alkawari Cikawa

Next Post

Mutane 6 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Ondo

Related

Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Har Da Na Amurka 
Daga Birnin Sin

Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Har Da Na Amurka 

18 hours ago
Hadin Gwiwar Sin Da Yankin Turai Na Kara Kawo Haske Ga Tattalin Arzikin Duniya
Daga Birnin Sin

Hadin Gwiwar Sin Da Yankin Turai Na Kara Kawo Haske Ga Tattalin Arzikin Duniya

19 hours ago
Yunkurin Philippines Bai Kai Gaci Ba A Tekun Kudancin Kasar Sin 
Daga Birnin Sin

Yunkurin Philippines Bai Kai Gaci Ba A Tekun Kudancin Kasar Sin 

20 hours ago
Kamfanoni Mallakin Gwamnatin Sin Sun Samu Bunkasa Bisa Daidaito Cikin Watanni Hudu Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Kamfanoni Mallakin Gwamnatin Sin Sun Samu Bunkasa Bisa Daidaito Cikin Watanni Hudu Na Farkon Bana

21 hours ago
Masu Bincike Na Sin Sun Cimma Sabon Sakamako A Fannin Saurin Sadarwa Tsakanin Tauraron Dan Adam Da Doron Duniya
Daga Birnin Sin

Masu Bincike Na Sin Sun Cimma Sabon Sakamako A Fannin Saurin Sadarwa Tsakanin Tauraron Dan Adam Da Doron Duniya

23 hours ago
An Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC
Daga Birnin Sin

An Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC

23 hours ago
Next Post
Mutane 6 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Ondo

Mutane 6 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Ondo

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Caccaki Gwamnatin Tinubu, Ya Yi Gargaɗi Kan Cin Sabon Bashi

Atiku Ya Caccaki Gwamnatin Tinubu, Ya Yi Gargaɗi Kan Cin Sabon Bashi

May 29, 2025
Ɗalibai Sun Rubuta Jarrabawar WAEC Cikin Dare A Duhu

Ɗalibai Sun Rubuta Jarrabawar WAEC Cikin Dare A Duhu

May 29, 2025
Zaman lafiya

MDD Ta Gudanar Da Bikin Ranar Tunawa Da Dakarun Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Duniya Ta 2025

May 29, 2025
Buhari Ya Yabi Tinubu, Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Rage Tsammani Da Dogon Buri

Buhari Ya Yabi Tinubu, Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Rage Tsammani Da Dogon Buri

May 29, 2025
Gwamnatin Kano Ta Fara Biyan Tsoffin Kansiloli Na APC Sama Da Naira Biliyan 16

Gwamnatin Kano Ta Fara Biyan Tsoffin Kansiloli Na APC Sama Da Naira Biliyan 16

May 29, 2025
Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Har Da Na Amurka 

Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Har Da Na Amurka 

May 28, 2025
Miƙa Mulki Daga Buhari Zuwa Tinubu: Abubuwan Da Suka Fi Jan Hankali

Tinubu Ya Yi Ƙoƙari, Gyaran Nijeriya Aikin Kowa Da Kowa Ne – Buhari

May 28, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Yankin Turai Na Kara Kawo Haske Ga Tattalin Arzikin Duniya

Hadin Gwiwar Sin Da Yankin Turai Na Kara Kawo Haske Ga Tattalin Arzikin Duniya

May 28, 2025
Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

May 28, 2025
Yunkurin Philippines Bai Kai Gaci Ba A Tekun Kudancin Kasar Sin 

Yunkurin Philippines Bai Kai Gaci Ba A Tekun Kudancin Kasar Sin 

May 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.