ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kyan Alkawari Cikawa

by CMG Hausa
4 years ago
Alkawari

Akwai wasu mutane 2, daya ya iya magana sosai, amma ya kan manta da maganar da ya fada, yayin da dayan ba ya son magana, sai dai duk wani alkawari da ya yi, zai yi kokarin cika shi.

A cikin mutanen nan 2 wanne ka fi so? Tabbas za a kulla abota tare da mutum na biyu ko? Saboda “Alkawari kaya ne”. Ba za a iya dogaro kan wani ba, idan ba zai iya cika alkawari ba.

  • Nasarorin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka A Shekaru Goman Baya

Wani babban dalilin da ya sa kasar Sin ta zama aminiyar kasashen Afirka, shi ne yadda suke iya dogaro da ita, wato yadda take kokarin cika alkawarin da ta yi.

ADVERTISEMENT

Don tabbatar da gaskiyar maganar, za mu iya kwatanta alkawarin da shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya yi, a taron ministocin dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka (FOCAC) da ya gudana a birnin Dakar na Senegal, a karshen shekarar 2021, da jawabin da ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya yi, wajen taron jami’ai masu kula da aiwatar da sakamakon taron ministoci na FOCAC, wanda ya gudana a kwanan baya, inda jami’in ya yi bayani kan yadda kasar Sin take kokarin cika alkawarinta.

A wajen taron Dakar, shugaba Xi ya ce kasar Sin za ta ba kamfanonin hada-hadar kudi na kasashen Afirka lamuni, na cin bashin da ya kai dala biliyan 10 cikin shekaru 3 masu zuwa.

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Zuwa yanzu watanni 8 sun wuce, an riga an ba da lamuni na samun bashin da ya kai dala biliyan 3. Ban da haka, kasar Sin ta ba da rance na dala biliyan 2.5, don tallafawa kokarin gudanar da wasu manyan ayyuka a kasashen Afirka.

A taron da ya gudana a bara, shugaba Xi ya ce kasar Sin za ta yi kokarin shigo da kayayyakin kirar kasashen Afirka da darajarsu za ta kai dala biliyan 300 cikin shekaru 3. Sa’an nan cikin watanni 7 da suka wuce, kasar Sin ta riga ta shigo da kayayyaki na dala biliyan 70.6 daga Afirka.

Yayin da a nasu bangare, kamfanonin Sin sun zuba jari da ya kai dala biliyan 2.17 ga kasuwannin kasashen Afirka, cikin watanni fiye da 8 da suka gabata.

A fannin aikin kiwon lafiya, shugaba Xi ya ce cikin shekaru 3, kasar Sin za ta ba da tallafin alluran rigakafin cutar COVID-19 miliyan 600 ga kasashen Afirka, haka kuma kamfanonin kasar da na kasashen Afirka, za su yi hadin gwiwa wajen samar da alluran rigakafin cutar COVID-19 miliyan 400.

Zuwa yanzu, wasu watanni 8 sun shude, kasar Sin ta riga ta ba da tallafin alluran rigakafin cutar COVID-19 miliyan 189 ga wasu kasashe 27 dake nahiyar Afirka, kana kamfanonin kasar ta yi kokarin hadin kai tare da takwarorinsu dake kasashen Afirka wajen sarrafa alluran, inda karfinsu ya kai samar da alluran rigakafi kimanin miliyan 400 a duk shekara.

Sauran ayyukan tallafi da hadin gwiwa da kasar Sin ta yi alkawarin aiwatar da su a kashen Afirka, sun hada da gina babban ginin hedkwatar cibiyar kandagarkin cututtuka ta nahiyar Afirka, da sauran manyan asibitocin hadin gwiwa, da rage talauci, da raya bangaren makamashi mai tsabta, da aikin tsaro, da dai sauransu, duk ana kokarin ciyar da su gaba, kamar yadda kasar Sin ta yi alkawari a baya.

Me ya sa kasar Sin take dora matukar muhimmanci kan cika alkawari? Saboda babbar manufar kasar Sin ta fuskar hadin gwiwa da kasashen Afirka ita ce, “gaskiya, da daukar takamaiman matakai, da zumunta, da sahihanci”, gami da “dora muimmanci kan adalci maimakon moriya”.

Kana Sin ta tsara wannan manufa ce bisa tushen akidarta ta “al’ummar dan Adam mai makomar bai daya”.

A ganin Sinawa, dole ne a yi kokarin tabbatar da ci gaban harkoki a kasashe daban daban, kafin a iya tabbatar da makomar bai daya mai haske ta daukacin dan Adam.

Wannan akida ta sa kasar Sin ke nuna cikakken sahihanci ga kasashen Afirka, da kokarin cika alkawarinta, yayin da take hulda da su. (Bello Wang)

Alkawari
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Next Post
Girmama Cikakken ’Yanci Da Yankunan Kasa, Wajibi Ne A Kan Kowacce Kasa Babba, Ko Karama

Girmama Cikakken ’Yanci Da Yankunan Kasa, Wajibi Ne A Kan Kowacce Kasa Babba, Ko Karama

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.