• English
  • Business News
Thursday, August 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Wajaba Amurka Ta Kaucewa Sake Maimaita Irin Kuskuren Da Ta Aikata Game Da Taiwan

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ya Wajaba Amurka Ta Kaucewa Sake Maimaita Irin Kuskuren Da Ta Aikata Game Da Taiwan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A duniyar yau, ba wanda ya zarce Amurka a fannin iya maida fari baki, da juyar da tunanin al’umma.

Kasa ce dake kan gaba wajen ta da husuma, da kin karbar kuskuren ta, da sauya matsaya da cin dunduniya, halayen da suka zamewa kasar dabi’a a duk lokacin da take cudanya da sassan kasa da kasa.

  • Akwai Alamun Ba Gudu Ba Ja Da Baya A Kan Batun Taiwan

To sai dai kuma, karya ba za ta tserewa gaskiya ba. Idan an kalli batun da ya shafi takaddamar zirin Taiwan, duk mai hankali zai fahimci abu ne da Amurka ta tsara domin yin tsokana.

Bisa nufinta na tabbatar da daidaito a zirin Taiwan, tun da wuri Sin ta bayyana rashin amincewa, da shirin ziyarar kakakin majalissar wakilan Amurka Nancy Pelosi, kasar Sin ta yi ta nanata mummunar illar da ziyarar ta Pelosi za ta haifar, da ma sakamakon da Amurkar za ta samu idan har Pelosi ta aiwatar da ziyarar, duk da kashedin da ya fito daga sassa daban daban.

Dokokin kasa da kasa, sun baiwa kasashe ikon mulkin kai da tsaron yankuna, kana sun haramtawa duk wata kasa tsoma baki cikin harkokin cikin gidan wata. Don haka, bisa kunnen kashe da Amurka ta yi, ta aikata mummunar ta’asa, kuma Sin ba ta da zabi, illa ta mayar da martani.

Labarai Masu Nasaba

Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci

Matakai daban daban da kasar Sin ta aiwatar domin mayar da martani ga waccan ziyara, na da nufin yin gargadi ne ga masu aikata ta’asa, ta yunkurin samar da ’yancin Taiwan.

Sin ta zartas da matakan kare babbar moriyarta bisa doka. Kuma matakan nata sun dace da dokokin kasa da kasa da na cikin gida.

Tun fil azal, yankin Taiwan bangare ne na kasar Sin. Kuma sakamakon tsokana daga waje, ya sa dakarun sojin kasar Sin suka gudanar da atisayen soji, da sarrafa makamai a yankunan tekun dake daura da tsibirin na Taiwan, a wani mataki na tabbatar da ikon mulkin kai, da tsaron yankunan Sin. Wannan kuma na kunshe ne cikin tanade-tanaden kundin mulkin kasar, da dokokin dake haramta yunkurin ballewa daga kasar, da ma sauran dokoki masu nasaba da hakan.

Manufar kasar Sin daya tak a duniya, muhimmiyar ka’ida ce da kasar Sin ke karewa. Don haka ya wajaba, Amurka ta koyi darasi daga matakin kuskure da Pelosi ta aikata, ta komawa hanya madaidaiciya, wadda za ta dace da manufar kasar Sin daya tak a duniya, da sanarwoyi 3 da sassan biyu suka sanyawa hannu.

Ya wajaba Amurka ta kaucewa kara yin wasu kura-kurai. Idan kuma ta ci gaba, Sin za ta maida martani yadda ya kamata. (Saminu Alhassan)

 

 

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Alluran Rigakafin COVID-19 Ta Haifar Da Kyakkyawan Sakamako

Next Post

Hukumar NDLEA Ta Cafke Wani Basarake Da Miyagun Kwayoyi A Jihar Sakkwato

Related

Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya
Daga Birnin Sin

Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

13 hours ago
Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci

14 hours ago
Adadin Cinikayyar Sin Da Kasashen Kungiyar SCO Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi
Daga Birnin Sin

Adadin Cinikayyar Sin Da Kasashen Kungiyar SCO Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi

17 hours ago
Jimilar Darajar Hada-Hadar Shige Da Fice A Fannin Bayar Da Hidimomi Ta Kasar Sin Ta Kai Yuan Tiriliyan 3.9 A Rabin Farko Na Shekarar Bana
Daga Birnin Sin

Jimilar Darajar Hada-Hadar Shige Da Fice A Fannin Bayar Da Hidimomi Ta Kasar Sin Ta Kai Yuan Tiriliyan 3.9 A Rabin Farko Na Shekarar Bana

17 hours ago
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

18 hours ago
Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama
Daga Birnin Sin

Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

19 hours ago
Next Post
Hukumar NDLEA Ta Cafke Wani Basarake Da Miyagun Kwayoyi A Jihar Sakkwato

Hukumar NDLEA Ta Cafke Wani Basarake Da Miyagun Kwayoyi A Jihar Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano

An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano

August 28, 2025
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

’Yansanda Sun Ceto Mutane 16 Da Aka Sace A Edo

August 28, 2025
Uwa Da ’Ya’yanta 3 Sun Rasu Bayan Gini Ya Rufta Musu A Zariya

Uwa Da ’Ya’yanta 3 Sun Rasu Bayan Gini Ya Rufta Musu A Zariya

August 28, 2025
ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A Zaɓen 2027 – Amaechi

ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A Zaɓen 2027 – Amaechi

August 28, 2025
Tinubu Ya Dawo Nijeriya Bayan Ziyarar Aiki A Brazil

Tinubu Ya Dawo Nijeriya Bayan Ziyarar Aiki A Brazil

August 28, 2025
Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

August 27, 2025
Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci

Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci

August 27, 2025
Yadda Aka Cafke Masu Saka Ƙwayoyi A Jakunkunan Matafiya A Filin Jirgin Sama A Kano

Yadda Aka Cafke Masu Saka Ƙwayoyi A Jakunkunan Matafiya A Filin Jirgin Sama A Kano

August 27, 2025
Adadin Cinikayyar Sin Da Kasashen Kungiyar SCO Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi

Adadin Cinikayyar Sin Da Kasashen Kungiyar SCO Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi

August 27, 2025
Jimilar Darajar Hada-Hadar Shige Da Fice A Fannin Bayar Da Hidimomi Ta Kasar Sin Ta Kai Yuan Tiriliyan 3.9 A Rabin Farko Na Shekarar Bana

Jimilar Darajar Hada-Hadar Shige Da Fice A Fannin Bayar Da Hidimomi Ta Kasar Sin Ta Kai Yuan Tiriliyan 3.9 A Rabin Farko Na Shekarar Bana

August 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.