• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Da Ya Daɗe Da Rasuwa Idan A Asibitocin Nijeriya Ake Duba Shi – Adesina

by Sadiq
2 months ago
in Manyan Labarai
0
Buhari Da Ya Daɗe Da Rasuwa Idan A Asibitocin Nijeriya Ake Duba Shi – Adesina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon mai bai wa tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, shawara kan harkokin yaɗa labarai, Femi Adesina, ya janyo ce-ce-ku-ce bayan da ya ce da Buhari ya dogara da asibitocin Nijeriya, da ya daɗe da rasuwa.

Adesina ya faɗi haka ne a wani shiri na musamman a gidan talabijin na Channels da aka gabatar domin tunawa da Buhari, wanda ya rasu a wani asibiti da ke Landan a ranar Lahadi.

  • HOTUNA: An Tsaurara Tsaro A Gidan Buhari Da Ke Daura
  • Ministan Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Rasha 

Wasu sun soki yadda Buhari ke yawan zuwa ƙasashen waje domin neman lafiya.

Amma Adesina ya kare shi, inda ya bayyana cewa Buhari ya daɗe yana zuwa asibiti a Landan tun kafin ya zama shugaban ƙasa a 2015.

“Likitocin can sun san rashin lafiyarsa sosai,” in ji Adesina.

Labarai Masu Nasaba

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

“Ba saboda wasa yake zuwa can ba, ya yarda da su, kuma sun san yadda za su kula da shi.”

Ya ƙara da cewa wasu daga cikin asibitocin Nijeriya ba su da kayan aiki da ƙwararrun ma’aikata da za su iya kula da lafiyar Buhari.

“In da ya dogara da wasu asibitocinmu, wataƙila da tuni ya riga mu gidan gaskiya,” in ji shi.

Wannan furuci ya ƙara jawo muhawara a faɗin ƙasar game da halin da harkar kiwon lafiya na Nijeriya ke ciki, da kuma yadda manyan ‘yan siyasa ke fita ƙetare don neman magani.

Buhari, ya shugabanci Nijeriya daga shekarar 2015 zuwa 2023.

A lokacin mulkinsa, musamman a shekarun farko, ya sha zuwa ƙasar Birtaniya domin neman lafiya, amma ba a taɓa bayyana cutar da ke damunsa ba.

Ya rasu ne a wani asibiti da ke Landan a ƙarshen mako, kuma mutuwarsa ta haifar da muhawara a faɗin ƙasar.

Za a gudanar da jana’izarsa a ranar Talata a Daura, a Jihar Katsina.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AdesinaAsibitiBuhariRasuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

HOTUNA: An Tsaurara Tsaro A Gidan Buhari Da Ke Daura

Next Post

Buhari Na Cikin Ƙoshin Lafiya Kwana Ɗaya Kafin Rasuwarsa – Mamman Daura

Related

Zamfara
Manyan Labarai

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 

2 minutes ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

2 hours ago
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja
Manyan Labarai

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

4 hours ago
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano
Manyan Labarai

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

6 hours ago
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba
Manyan Labarai

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

19 hours ago
Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?
Manyan Labarai

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

23 hours ago
Next Post
Buhari Na Cikin Ƙoshin Lafiya Kwana Ɗaya Kafin Rasuwarsa – Mamman Daura

Buhari Na Cikin Ƙoshin Lafiya Kwana Ɗaya Kafin Rasuwarsa – Mamman Daura

LABARAI MASU NASABA

Zamfara

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 

September 15, 2025
Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

September 15, 2025
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

September 15, 2025
Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

September 15, 2025
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

September 15, 2025
Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

September 15, 2025
Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

September 15, 2025
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.