ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

by Sadiq
5 months ago
PDP

Fitaccen ɗan jaridar nan kuma mawallafin mujallar Ovation, Dele Momodu, ya bayyana cewa ya fice daga Jam’iyyar PDP tare da komawa jam’iyyar ADC.

A cikin wata wasiƙar da ya rubuta a ranar 17 ga watan Yuli, 2025, wacce ya aike wa Shugaban PDP na mazaɓar Ihievbe, ƙaramar hukumar Owan East ta Jihar Edo.

  • Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara
  • Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila

Momodu ya ce ya fice daga jam’iyyar ne saboda ta faɗa hannun masu adawa da dimokuraɗiyya.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana cewa yanzu zai mara wa jam’iyyar  ADC baya, wacce ke son ƙwace mulki daga hannun Shugaba Bola Tinubu da jam’iyyar APC a zaɓen 2027.

“Ina sanar da ku cewa na fice daga jam’iyyar PDP daga yau,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

“Dalilina kuwa yana da sauƙi. Jam’iyyar ta faɗa hannun masu adawa da dimokuraɗiyya.

“Saboda haka, abin da ya dace shi ne a bar musu ragowar jam’iyyar, yayin da mu da yawa za mu koma sabuwar jam’iyyar haɗaka mai suna ADC.”

A farkon wannan wata, Momodu ya zargi Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, da yi wa jam’iyyar APC aiki a ɓoye duk da kasancewarsa ɗan jam’iyyar PDP a lokacin zaɓen shugaban ƙasa na 2023.

Ya ce: “Ba tare da wata shakka ba, mutane suna bar wa Wike da abokan aikinsa PDP. Wannan lamari an riga an hango shi. Jam’iyyar APC mai mulki tana shigar da mutanenta a manyan jam’iyyun adawa don tarwatsa su.”

Haka kuma, Momodu ya caccaki gwamnatin Bola Tinubu, yana cewa tana ƙara jefa rayuwar ‘yan Nijeriya cikin ƙunci fiye da yadda aka gani a lokacin tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari.

“Shin wannan ita ce Nijeriya da kuke mafarki? Rayuwarku ta fi ta da sauƙi ne fiye da shekaru biyu da suka wuce? Ko da Buhari ya tafi, mun ga abin da ya bari, amma yanzu lamarin ya ƙara muni,” in ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani
Manyan Labarai

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Next Post
Kano Pillars Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Gidan Rediyon RFI Hausa

Kano Pillars Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Gidan Rediyon RFI Hausa

LABARAI MASU NASABA

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.