ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

by Sadiq
11 months ago
PDP

Fitaccen ɗan jaridar nan kuma mawallafin mujallar Ovation, Dele Momodu, ya bayyana cewa ya fice daga Jam’iyyar PDP tare da komawa jam’iyyar ADC.

A cikin wata wasiƙar da ya rubuta a ranar 17 ga watan Yuli, 2025, wacce ya aike wa Shugaban PDP na mazaɓar Ihievbe, ƙaramar hukumar Owan East ta Jihar Edo.

  • Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara
  • Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila

Momodu ya ce ya fice daga jam’iyyar ne saboda ta faɗa hannun masu adawa da dimokuraɗiyya.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana cewa yanzu zai mara wa jam’iyyar  ADC baya, wacce ke son ƙwace mulki daga hannun Shugaba Bola Tinubu da jam’iyyar APC a zaɓen 2027.

“Ina sanar da ku cewa na fice daga jam’iyyar PDP daga yau,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Tinubu Ya Ba Da Umarnin Tsaurara Tsaro A NIPSS Bayan Harin ’Yan Bindiga

“Dalilina kuwa yana da sauƙi. Jam’iyyar ta faɗa hannun masu adawa da dimokuraɗiyya.

“Saboda haka, abin da ya dace shi ne a bar musu ragowar jam’iyyar, yayin da mu da yawa za mu koma sabuwar jam’iyyar haɗaka mai suna ADC.”

A farkon wannan wata, Momodu ya zargi Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, da yi wa jam’iyyar APC aiki a ɓoye duk da kasancewarsa ɗan jam’iyyar PDP a lokacin zaɓen shugaban ƙasa na 2023.

Ya ce: “Ba tare da wata shakka ba, mutane suna bar wa Wike da abokan aikinsa PDP. Wannan lamari an riga an hango shi. Jam’iyyar APC mai mulki tana shigar da mutanenta a manyan jam’iyyun adawa don tarwatsa su.”

Haka kuma, Momodu ya caccaki gwamnatin Bola Tinubu, yana cewa tana ƙara jefa rayuwar ‘yan Nijeriya cikin ƙunci fiye da yadda aka gani a lokacin tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari.

“Shin wannan ita ce Nijeriya da kuke mafarki? Rayuwarku ta fi ta da sauƙi ne fiye da shekaru biyu da suka wuce? Ko da Buhari ya tafi, mun ga abin da ya bari, amma yanzu lamarin ya ƙara muni,” in ji shi.

MASU ALAKA

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa
Manyan Labarai

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ba Da Umarnin Tsaurara Tsaro A NIPSS Bayan Harin ’Yan Bindiga

June 19, 2026
Kotun Ƙoli Za Ta Yanke Hukunci Kan Rikicin PDP Da ADC Yau
Siyasa

Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina

June 19, 2026
Next Post
Kano Pillars Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Gidan Rediyon RFI Hausa

Kano Pillars Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Gidan Rediyon RFI Hausa

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Abinci

Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma

June 19, 2026
Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

June 19, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

June 19, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

June 19, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

June 19, 2026
Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

June 19, 2026
Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

June 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.