• English
  • Business News
Tuesday, August 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dole Mu Hada Kai Da ‘Yan Siyasa Don Ciyar Da Masana’antar Kannywood Gaba -Shugaban MOPPAN

by Rabilu Sanusi Bena, Sulaiman and Rabilu Sani Bena
3 weeks ago
in Labarai
0
Dole Mu Hada Kai Da ‘Yan Siyasa Don Ciyar Da Masana’antar Kannywood Gaba -Shugaban MOPPAN
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sabon shugaban riko na kungiyar masu shirya fina-finai ta Nijeriya (MOPPAN), Alhaji Shehu Hassan Kano ya bayyana cewa; yanzu lokaci ne da ya kamata masana’antar Kannywood ta hada kai da ‘yan siyasa, musamman wadanda ke rike da mulki; domin sama wa masana’antar ci gaba mai dorewa, a wata hira da ya yi da FIM, Shehu Hassan, wanda shi ne ya maye gurbin tsohon shugaban kungiyar, Malam Mai Kudi (Cashman), wanda ya rasu a kwanakin baya ya bayyana cewa; kowa da kowa nasu ne a MOPPAN.

“Ba jam’iyya za mu shiga ba, ba kuma wani bangare na siyasa za mu yi ba, ita masana’antar Kannywood, akwai ‘yan siyasa, kuma ba jam’iyya daya suke yi ba, za ka ga wasu suna wannan jam’iyar; yayin da wasu kuma za su zabi wata jam’iyyar daban, don haka, mu a tsarinmu na MOPPAN, kowa namu ne, dan masana’antarmu ne, duk wanda ya ga akwai wani abu da za a yi harkar fim ta ci gaba, ya kawo mana shi, mu nan a kungiyance za mu shige gaba wajen ganin wannan abu ya tabbata”, in ji Hassan Kano.

  • Wace Kasa Ce Take Son Zama “Kasa Ta Uku Mai Tsaro” A Wurin Amurka?
  • Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

Har ila yau, ya ci gaba da bayyana cewa; don haka, mu ba wani bangare guda daya za mu bi mu rike ba, domin kuwa yin hakan; akwai hadari, so muke in dai dan fim ne, duk wata tafiya da yake yi ta siyasa; ya zamana ya amfana da tafiyar, ita ma masana’antar ta amfana, ko da kuwa ba jam’iyyarsa ba ce take mulki, za mu hadu ne a matsayin ‘yan fim mu amfana da junanmu a wajen tafiyar siyasa.

Wannnan na zuwa ne a daidai lokacin da aka fara kada gangar siyasa a Nijeriya, kwanaki dai an hangi wasu jarumai a masana’antar Kannywood, sun kai ziyara har gida ga tsohon mataimakin shugaban kasa, kuma tsohon dan takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyar PDP, a babban zaben da ya gabata, Alhaji Atiku Abubakar (Wazirin Adamawa).

Hakan yasa wasu ke ganin hakan bai dace ba, ganin cewa; Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ta bugi kirjin yi wa masana’antar Kannywood gata, ta hanyar bai wa wasu daga cikin jaruman masana’antar Kannywood manya-manyan mukamai a gwamnati, ciki har da Babban Manajin Darakta na Hukumar Fina-finai ta Nijeriya (NFC).

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Ta Bayar Da Kwangilar Hanyoyi 17 Akan Naira Biliyan 40.8

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

Koma dai mene ne, Shehu Hassan Kano ya ce; ba za su takurawa kowa a cikin ‘yan kungiyar ta MOPPAN, wajen yin ra’ayin siyasar da suka ga dama ba, sai dai, ya ce duk wanda zai yi siyasa ya fara dubawa idan akwai mafita, sai ya shiga idan kuma babu sai ya hakura ya canza wata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xia Xueying: Muna Sayo Kashi 90% Na Kayan Aikinmu Daga Kasar Sin

Next Post

Kasar Sin Ta Ba Da Rahoton Samun Ci Gaban Aikin Gona Mara Gurbata Muhalli Ba Tare Da Tangarda Ba

Related

Kano
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Bayar Da Kwangilar Hanyoyi 17 Akan Naira Biliyan 40.8

9 minutes ago
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi
Manyan Labarai

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

3 hours ago
An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami
Manyan Labarai

An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami

5 hours ago
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

Jagora A ADC Ya Ƙaryata Zargin Atiku Ya Kankane Komai A Jam’iyyar

6 hours ago
’Yan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 6 A Taraba
Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 6 A Taraba

7 hours ago
Ba Iya Yunwa Ce Kaɗai Ke Kashe Ƙananan Yara A Katsina Ba – Gwamnati
Labarai

Ba Iya Yunwa Ce Kaɗai Ke Kashe Ƙananan Yara A Katsina Ba – Gwamnati

9 hours ago
Next Post
Kasar Sin Ta Ba Da Rahoton Samun Ci Gaban Aikin Gona Mara Gurbata Muhalli Ba Tare Da Tangarda Ba

Kasar Sin Ta Ba Da Rahoton Samun Ci Gaban Aikin Gona Mara Gurbata Muhalli Ba Tare Da Tangarda Ba

LABARAI MASU NASABA

Kano

Gwamnatin Kano Ta Bayar Da Kwangilar Hanyoyi 17 Akan Naira Biliyan 40.8

August 12, 2025
Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

August 12, 2025
‘Yan Nijeriya Miliyan 14 Sun Yi Bikin Murnar Karɓar Kyautar N23m Daga Bankin STANBIC IBTC

‘Yan Nijeriya Miliyan 14 Sun Yi Bikin Murnar Karɓar Kyautar N23m Daga Bankin STANBIC IBTC

August 12, 2025
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

August 12, 2025
An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami

An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami

August 12, 2025
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

Jagora A ADC Ya Ƙaryata Zargin Atiku Ya Kankane Komai A Jam’iyyar

August 12, 2025
’Yan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 6 A Taraba

’Yan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 6 A Taraba

August 12, 2025
Sadiq Umar Da Bello El-Rufai Sun Sayi Ƙungiyar Rancher Bees FC Ta Kaduna

Sadiq Umar Da Bello El-Rufai Sun Sayi Ƙungiyar Rancher Bees FC Ta Kaduna

August 12, 2025
Ba Iya Yunwa Ce Kaɗai Ke Kashe Ƙananan Yara A Katsina Ba – Gwamnati

Ba Iya Yunwa Ce Kaɗai Ke Kashe Ƙananan Yara A Katsina Ba – Gwamnati

August 12, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Batun Rashin Lafiyar Tinubu

August 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.