ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wace Kasa Ce Take Son Zama “Kasa Ta Uku Mai Tsaro” A Wurin Amurka?

by CGTN Hausa and Sulaiman
11 months ago
Amurka

A baya-bayan nan ne dai ministan harkokin wajen Najeriya Yusuf Tuggar ya fito fili ya bayyana cewa, Amurka na yin matsin lamba ga kasashen Afirka, don su karbi bakin hauren da Amurka ta kora daga cikin gidanta. Inda Najeriya, a bisa matsayinta na wata babbar kasa, ta daure da matsin lambar, kuma ta ce “A’a” ga Amurka. Sai dai ga wasu kasashe masu raunin tattalin arziki, da suke fuskantar matsin lamba daga Amurka, yawancinsu ba su da wani zabi illa mika wuya.

A cewar gidan telabijin na CNN, a kwanan baya kasar Amurka ta kori bakin haure biyar, ‘yan kasashen Jamaica, Laos, Cuba, Yemen da Vietnam, wadanda ake zargi da aikata manyan laifuffuka a kasar. Sa’an nan ta tusa keyarsu zuwa kasar da take wa lakabin “kasa ta uku mai tsaro”, wato kasar Eswatini dake kudancin nahiyar Afirka. Wannan lamari dai ya haifar da fushi mai tsanani a tsakanin al’ummar Eswatini. Har ma jam’iyyar adawa ta kasar, PUDEMO, ta ce karbar wadannan bakin haure da Amurka ta kora “yana da babbar barazana ga al’ummar Eswatini, wadanda da ma sun kasance cikin yanayi mai rauni.”

  • An Samu Rarrabuwar Kai Kan Makin Shiga Manyan Makarantu
  • Yadda Hauhawar Farashin Kayan Abinci Ya Ragu A Nijeriya

Abin da ya ba ni sha’awa a cikin wannan al’amari shi ne sunan da Amurka ta lakaba wa Eswatini, wato “kasa ta uku mai tsaro”. A cewar wasu takardun bayani na kungiyar kasashen Turai ta EU, kukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya ta taba jaddada cewa, ya kamata a sami “alaka mai ma’ana” tsakanin “kasa ta uku mai tsaro” da ‘yan gudun hijira masu neman mafaka, misali, dangin da ke zaune a kasar. Bugu da kari, ya kamata “kasa ta uku mai tsaro” ta tabbatar da cewa ‘yan gudun hijirar sun sami cikakkiyar kariya a cikin yankunanta.

ADVERTISEMENT

Bisa ga wannan ma’auni, bai kamata a dora Eswatini a matsayin “kasa ta uku mai tsaro” ba. Saboda, da farko, babu wata “alaka mai ma’ana” tsakanin mutanen biyar da kasar Eswatini. Na biyu, da alama kasar ba za ta iya ba wa wadannan mutane “cikakkiyar kariya” ba. Bisa wani rahoton batun kare hakkin dan Adam na kasar Eswatini da ma’aikatar harkokin wajen kasar Amurka ta fitar, an ce akwai lamarin “aikata hukuncin kisa ba bisa doka ba” da “hukunce-hukunce na zalunci” da suka afku a kasar, kuma gidajen yarin kasar na fuskantar matsalolin “cunkoso, da lalacewar kayayyaki, da rashin abinci mai gina jiki, da yawan samun fadace-fadace tsakanin fursunoni.”

Amma duk da haka kasar Amurka ta mai da Eswatini a matsayin “kasa ta uku mai tsaro”. Saboda me? Dalili na farko shi ne domin kasar Amurka ta ga yana da sauki a sarrafa wata karamar kasa, wadda za ta karbi bakin hauren da aka kora, bayan an dan matsa mata lamba. Bugu da kari, wata takardar gwamnati da jaridar Washington Post ta nuna wa jama’a ta shaida ce, watakila da gangan ne gwamnatin Amurka ke korar bakin haure zuwa kasashen da ba a samun cikakken hakkin dan Adam. Ta haka ne gwamnatin Amurka ke fatan tilasta wa bakin haure don su bar kasar da kansu, in ba haka ba za a iya korarsu zuwa Eswatini, ko kuma Sudan ta Kudu da ke fama da tashin hankali, har ma za a iya kulle su a rumbun ajiyar kaya na wani sansanin sojan Amurka dake nahiyar Afirka (wani abu da ya taba faruwa a kasar Djibouti a baya-bayan nan) .

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

Ana iya takaita halin Amurka game da wannan al’amari da kalma daya: Maras kulawa. Saboda kasar ba ta damu da nauyin da ke kanta bisa la’akari da matsayinta na babbar kasa ba, balle ma dangantakar diflomasiyya, da adalci, da hakkin bil’adama, da muradu na wasu kasashe. Sai dai abu daya kawai dake janyo hankalinta, wato kokarin cika burin korar baki. Hakika wannan ra’ayi na “Amurka na gaba da kome” da yanayi na son kai sun kasance cikin dukkan manufofin kasar.

Eswatini, wadda Amurka ta manna ta kan matsayin “kasa ta uku mai tsaro” a wannan karo, ba a san irin “yarjejeniya” da ta kulla da Amurka ba. Amma, zai yi matukar wahala Eswatini ta kare muradunta, yayin da take mu’amala da wata babbar kasa kamar Amurka mai matukar son kai. (Bello Wang)

Amurka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya
Amurka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware
  • Sulaiman
    Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma
  • Sulaiman
    Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin
  • Sulaiman
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

MASU ALAKA

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Daga Taklamakan Zuwa Sahara: Yadda Hamada Ke “Haifar” Da Fata
Ra'ayi Riga

Daga Taklamakan Zuwa Sahara: Yadda Hamada Ke “Haifar” Da Fata

June 17, 2026
Next Post
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Abinci

Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma

June 19, 2026
Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

June 19, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

June 19, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

June 19, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

June 19, 2026
Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

June 19, 2026
Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

June 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.