ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wace Kasa Ce Take Son Zama “Kasa Ta Uku Mai Tsaro” A Wurin Amurka?

by CGTN Hausa and Sulaiman
12 months ago
Amurka

A baya-bayan nan ne dai ministan harkokin wajen Najeriya Yusuf Tuggar ya fito fili ya bayyana cewa, Amurka na yin matsin lamba ga kasashen Afirka, don su karbi bakin hauren da Amurka ta kora daga cikin gidanta. Inda Najeriya, a bisa matsayinta na wata babbar kasa, ta daure da matsin lambar, kuma ta ce “A’a” ga Amurka. Sai dai ga wasu kasashe masu raunin tattalin arziki, da suke fuskantar matsin lamba daga Amurka, yawancinsu ba su da wani zabi illa mika wuya.

A cewar gidan telabijin na CNN, a kwanan baya kasar Amurka ta kori bakin haure biyar, ‘yan kasashen Jamaica, Laos, Cuba, Yemen da Vietnam, wadanda ake zargi da aikata manyan laifuffuka a kasar. Sa’an nan ta tusa keyarsu zuwa kasar da take wa lakabin “kasa ta uku mai tsaro”, wato kasar Eswatini dake kudancin nahiyar Afirka. Wannan lamari dai ya haifar da fushi mai tsanani a tsakanin al’ummar Eswatini. Har ma jam’iyyar adawa ta kasar, PUDEMO, ta ce karbar wadannan bakin haure da Amurka ta kora “yana da babbar barazana ga al’ummar Eswatini, wadanda da ma sun kasance cikin yanayi mai rauni.”

  • An Samu Rarrabuwar Kai Kan Makin Shiga Manyan Makarantu
  • Yadda Hauhawar Farashin Kayan Abinci Ya Ragu A Nijeriya

Abin da ya ba ni sha’awa a cikin wannan al’amari shi ne sunan da Amurka ta lakaba wa Eswatini, wato “kasa ta uku mai tsaro”. A cewar wasu takardun bayani na kungiyar kasashen Turai ta EU, kukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya ta taba jaddada cewa, ya kamata a sami “alaka mai ma’ana” tsakanin “kasa ta uku mai tsaro” da ‘yan gudun hijira masu neman mafaka, misali, dangin da ke zaune a kasar. Bugu da kari, ya kamata “kasa ta uku mai tsaro” ta tabbatar da cewa ‘yan gudun hijirar sun sami cikakkiyar kariya a cikin yankunanta.

ADVERTISEMENT

Bisa ga wannan ma’auni, bai kamata a dora Eswatini a matsayin “kasa ta uku mai tsaro” ba. Saboda, da farko, babu wata “alaka mai ma’ana” tsakanin mutanen biyar da kasar Eswatini. Na biyu, da alama kasar ba za ta iya ba wa wadannan mutane “cikakkiyar kariya” ba. Bisa wani rahoton batun kare hakkin dan Adam na kasar Eswatini da ma’aikatar harkokin wajen kasar Amurka ta fitar, an ce akwai lamarin “aikata hukuncin kisa ba bisa doka ba” da “hukunce-hukunce na zalunci” da suka afku a kasar, kuma gidajen yarin kasar na fuskantar matsalolin “cunkoso, da lalacewar kayayyaki, da rashin abinci mai gina jiki, da yawan samun fadace-fadace tsakanin fursunoni.”

Amma duk da haka kasar Amurka ta mai da Eswatini a matsayin “kasa ta uku mai tsaro”. Saboda me? Dalili na farko shi ne domin kasar Amurka ta ga yana da sauki a sarrafa wata karamar kasa, wadda za ta karbi bakin hauren da aka kora, bayan an dan matsa mata lamba. Bugu da kari, wata takardar gwamnati da jaridar Washington Post ta nuna wa jama’a ta shaida ce, watakila da gangan ne gwamnatin Amurka ke korar bakin haure zuwa kasashen da ba a samun cikakken hakkin dan Adam. Ta haka ne gwamnatin Amurka ke fatan tilasta wa bakin haure don su bar kasar da kansu, in ba haka ba za a iya korarsu zuwa Eswatini, ko kuma Sudan ta Kudu da ke fama da tashin hankali, har ma za a iya kulle su a rumbun ajiyar kaya na wani sansanin sojan Amurka dake nahiyar Afirka (wani abu da ya taba faruwa a kasar Djibouti a baya-bayan nan) .

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

Ana iya takaita halin Amurka game da wannan al’amari da kalma daya: Maras kulawa. Saboda kasar ba ta damu da nauyin da ke kanta bisa la’akari da matsayinta na babbar kasa ba, balle ma dangantakar diflomasiyya, da adalci, da hakkin bil’adama, da muradu na wasu kasashe. Sai dai abu daya kawai dake janyo hankalinta, wato kokarin cika burin korar baki. Hakika wannan ra’ayi na “Amurka na gaba da kome” da yanayi na son kai sun kasance cikin dukkan manufofin kasar.

Eswatini, wadda Amurka ta manna ta kan matsayin “kasa ta uku mai tsaro” a wannan karo, ba a san irin “yarjejeniya” da ta kulla da Amurka ba. Amma, zai yi matukar wahala Eswatini ta kare muradunta, yayin da take mu’amala da wata babbar kasa kamar Amurka mai matukar son kai. (Bello Wang)

Amurka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Asusun IMF Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya, Ya Kuma Kara Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Alkaluman Farashin Kayayyakin Masarufi Na Kasar Sin Sun Karu Da Kaso 1 A Watan Yuni
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Taron Intanet Na Sin Karo Na 25 Ya Bayyana Yadda Ake Amfani Da Fasahar AI A Rayuwar Yau Da Kullum
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tunanin Xi Jinping kan JKS: Hikimar Mulki Ta Farfado Da Kasa Da Kuma Tasirinta A Duniya
Amurka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Asusun IMF Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya, Ya Kuma Kara Na Sin
  • Sulaiman
    Alkaluman Farashin Kayayyakin Masarufi Na Kasar Sin Sun Karu Da Kaso 1 A Watan Yuni
  • Sulaiman
    ‘Yansandan Jihohi Za Su Bai Wa Gwamnoni Cikakken Iko Wajen Yaƙi Da Matsalar Tsaro — Gwamna Dauda
  • Sulaiman
    Taron Intanet Na Sin Karo Na 25 Ya Bayyana Yadda Ake Amfani Da Fasahar AI A Rayuwar Yau Da Kullum

MASU ALAKA

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
Next Post
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

LABARAI MASU NASABA

Taƙaddamar Kafa Hukumar Bogi: Tinubu Ya Umarci A Yi Binciken Ƙwaƙwaf

Taƙaddamar Kafa Hukumar Bogi: Tinubu Ya Umarci A Yi Binciken Ƙwaƙwaf

July 10, 2026
Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

July 10, 2026
Asusun IMF Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya, Ya Kuma Kara Na Sin

Asusun IMF Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya, Ya Kuma Kara Na Sin

July 9, 2026
Alkaluman Farashin Kayayyakin Masarufi Na Kasar Sin Sun Karu Da Kaso 1 A Watan Yuni

Alkaluman Farashin Kayayyakin Masarufi Na Kasar Sin Sun Karu Da Kaso 1 A Watan Yuni

July 9, 2026
‘Yansandan Jihohi Za Su Bai Wa Gwamnoni Cikakken Iko Wajen Yaƙi Da Matsalar Tsaro — Gwamna Dauda

‘Yansandan Jihohi Za Su Bai Wa Gwamnoni Cikakken Iko Wajen Yaƙi Da Matsalar Tsaro — Gwamna Dauda

July 9, 2026
Taron Intanet Na Sin Karo Na 25 Ya Bayyana Yadda Ake Amfani Da Fasahar AI A Rayuwar Yau Da Kullum

Taron Intanet Na Sin Karo Na 25 Ya Bayyana Yadda Ake Amfani Da Fasahar AI A Rayuwar Yau Da Kullum

July 9, 2026
Tunanin Xi Jinping kan JKS: Hikimar Mulki Ta Farfado Da Kasa Da Kuma Tasirinta A Duniya

Tunanin Xi Jinping kan JKS: Hikimar Mulki Ta Farfado Da Kasa Da Kuma Tasirinta A Duniya

July 9, 2026
Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro

July 9, 2026
Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Kasar Sin Na Kara Samun Tagomashi A Kasuwannin Duniya

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Kasar Sin Na Kara Samun Tagomashi A Kasuwannin Duniya

July 9, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ɗaga Albashin Sojoji Daga Naira 49,000 Zuwa Naira 100,000 – Ministan Tsaro

Gwamnatin Tarayya Ta Ɗaga Albashin Sojoji Daga Naira 49,000 Zuwa Naira 100,000 – Ministan Tsaro

July 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.