• English
  • Business News
Thursday, July 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Janye ‘Yansandan Da Ke Aikin Kare Masu Hannu Da Shuni

by Leadership Hausa
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Kirsimeti: An Tsaurara Tsaro A Kwara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanan nan ne Karamar Ministar harkokin ‘Yansanda, Imaan Suleiman Ibrahim, ta sanar da umarnin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu na janye jami’an ‘yansanda da ke aikin kare masu hannu da shuni a fadin tarayyar kasar nan tare da sauya musu wurin aiki nan take ba tare da bata lokaci ba.

Ta kuma bayyana cewa, a cikin umarnin a kwai shirin samar da tsarin tabbatar da tsaro a unguwanni. Mun yi murnar samar da jami’an tsaro a cikin al’umma a matsayin mataki na yaki da masu aikata laifuka a sassan kasar nan.

  • Sanata Kaka Lawan Ya Gabatar Da Kudirin Tattara Dokokin Nijeriya Na Tsawon Shekara 19
  • Zaben Kano: ‘Yansanda Da Masu Zanga-zanga Sun Yi Arangama A Kano

Samar da tsaro ta hanyar amfani da al’umma yana daga cikin abubuwan da ake tattaunawa a tarukan jama’a na tsawon lokaci ana kuma ganinsa a matsayin wani mataki da zai kawo karshen matsalar tsaron da ake fuskanta wadda take dada karuwa a kullum musamman a yankunan karkara inda masu garkuwa da mutane da ‘yan bindiga ke gallaza wa al’umma.

Amma kafin mu koma ga irin wannan tsarin samar da tsaron bari mu koma a kan maganar yadda jami’an tsaro ke bayar da kariya ga masu hannu da shuni a cikin al’umma, lamarin da ya munana ta yadda duk wani mai kudi a aljihunsa kuma zai iya biya sai ya nemi ‘yansanda su rika ba shi kariya.

Wani tsohon shugaban hukumar kula da aikin ‘yansanda, kuma tsohon shugaban rundunar ‘yansandan Nijeriya, Mista Mike Okiro, ya yi gargadi a kan yadda wasu ‘yan kalilan da ya kwatanta da masu hannu da shuni da kuma wasu ‘yan kadan daga cikin al’umma suke amfani da jami’an ‘yansanda fiye da 150,000 don biyan bukatun kansu.

Labarai Masu Nasaba

Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

Tinubu Ya Tsawaita Wa’adin Shugaban Kwastan Da Shekara Ɗaya

Ya kuma ce, kasar nan ba za ta iya daukar yadda kusan rabin jami’an rundunar ‘yansanda ke aiki a hannun wasu mutane masu zaman kansu ba. Ya kuma yi korafin cewa, rundunar ‘yansanda ta kasa aiwatar da dokar janye jami’an ‘yansanda daga hidimta wa masu hannu da shuni ne saboda rashin kudi. Abin da wannan ke nufi shi ne wannan umarnin na Shugaban Kasa Tinubu na baya-bayan nan ba wai sabo ba ne, an sha bayar da irin wannan umarnin a baya amma masu amfana da al’amarin sun kasa bari a aiwatar da dokar.

Amma kuma ba wani sirri ba ne cewa, matsalar rundunar ‘yansandan Nijeriya wata aba ce da za a kwatanta da sarkakiyar kasar gaba daya. Duk da cewa, babbar matsalar da rundunar ke fuskanta ta shafi kudin gudanar da aiki amma kuma suna fuskantar karancin ma’aikata da za su taimaka musu kare al’umma yadda ya kamata, lamarin samar masu da kudi yana da muhimmaci amma shin wai rashin kudi ne matsalar ‘yansanda ko cin hanci da rashawa?.

Idan za a iya tunawa da al’amarin tsohon shugaban rundunar ‘yansada Tafa Balogun, hukumar EFCC ta tabbatar da ya sace fiye da naira Biliyan 16 cikin kudaden gudanar da rundunar.

Rundunar ‘yansandan Nijeriya a matsayinta ta daya daga cikin rundunonin tsaron kasar nan ya kamata ta bayar da muhimmanci ga rigakafin aukuwa da kuma gano masu shirin aikata laifuka ba wai su bar jami’anta na aikin kare wasu kalilan masu hannun da shuni ba a cikin al’umma.

A matsayin rundunar na hukuma mai aikin tabbatar da doka da oda, an dora wa rundunar aikin kare rayuka da dukiyiyoyin al’umma Nijeriya a duk inda suke a fadin kasar nan. Suna kuma yin haka ne ta hanyar aikawa da jami’ansu da sauran kayan aiki wurare masu muhimmanci don kare su daga ayyuykan bata gari. Haka kuma yana daga cikin ayyukan ‘yansanda samar da tsaro ga manyan ma’aikatan gwamnati da kuma manyan mutane da ke aikin gwamnati. Wannan abin da za a iya fahimta ne don wadanda ake karewa za su samu tabbacin suna da kariya a yayin da suke gudanar da aikinsu na yi wa kasa hidima.

Al’umma sun damu da ganin abin da ya kamata ya zama alfarma sai gashi an lalata shi, inda a halin yanzu jam’ai fiye da 150,000 maza da mata ke aikin kare wasu ‘yan kalilan a gidaje da ofishoshinsu na aiki, to lalai wannan ba abin da za a amince da shi ba ne.

A ra’ayijnmu ya kamata a janye ‘yansanda daga aikin ba da tsaro ga mutane da ba jami’an gwamnati ba ne, kuma da sauran masu hannun da shuni ya kamata a rage yawan jami’an ‘yansanda da ke aiki da su. A wasu lokutan sai a tura ‘yansanda fiye da biyar don gadin jami’in gwamnati daya, to lallai wannan ba abin a amince da shi ba ne.

Ba zai yiwu kasa ta yi ta fama da karancin jami’an ‘yansanda ba amma wasu da dama daga cikin jami’anta na can suna aikin kare wasu masu hannu da shuni. Don fuskantar matsalolin tsaron da ake fama da su a kasa, muna kira ga gwamnati da ta gaggauta kamma aikin daukar karin jami’an ‘yansanda a kuma tabbatar da suna yi wa kasa aiki ne ba wasu tsiraru ba.

Haka kuma wannan jaridar ta yi imani da cewa, ya kamata a tabbatar da an samar wa rundunar ‘yansanda isassun kudi da kayan aiki na zamani in har ana son su yi aiki yadda ya kamata kamar yadda ‘yansanda ke aiki a wasu kasashen duniya da suka ci gaba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murna Ga Baje Kolin Cinikayyar Digital Na Kasa Da Kasa Karo Na Biyu

Next Post

Zargin Kafar Angulu Ga Dimokuradiyyar Nijeriya: Cacar Baki Ta Barke Tsakanin ‘Yan Adawa Da Gwamnati

Related

Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

5 hours ago
Tinubu Ya Tsawaita Wa’adin Shugaban Kwastan Da Shekara Ɗaya
Manyan Labarai

Tinubu Ya Tsawaita Wa’adin Shugaban Kwastan Da Shekara Ɗaya

6 hours ago
Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC
Manyan Labarai

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC

12 hours ago
Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya
Manyan Labarai

Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya

15 hours ago
Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC
Manyan Labarai

Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC

1 day ago
Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana

1 day ago
Next Post
Zargin Kafar Angulu Ga Dimokuradiyyar Nijeriya: Cacar Baki Ta Barke Tsakanin ‘Yan Adawa Da Gwamnati

Zargin Kafar Angulu Ga Dimokuradiyyar Nijeriya: Cacar Baki Ta Barke Tsakanin 'Yan Adawa Da Gwamnati

LABARAI MASU NASABA

Yadda Yajin Aikin Ma’aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato

Yadda Yajin Aikin Ma’aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato

July 31, 2025
Zargin Da Wasu ’Yan Siyasar Amurka Ke Yi Wa Sin Na Fitar Da Hajoji Fiye Da Kima Ya Sabawa Hujjoji Na Hakika

Zargin Da Wasu ’Yan Siyasar Amurka Ke Yi Wa Sin Na Fitar Da Hajoji Fiye Da Kima Ya Sabawa Hujjoji Na Hakika

July 31, 2025
Gwamnatin Borno Ta Nada Kwamitin Aiwatar Da Mafi Karancin Albashi

Gwamna Zulum Ya Sauke Kwamishinoni Biyu Tare Da Maye Gurbinsu Da Wasu

July 31, 2025
Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka

Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka

July 31, 2025
Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

July 31, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Kyautata Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Hidimomin Dijital Da Na Kirkirarriyar Basira

Sin Na Ci Gaba Da Kyautata Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Hidimomin Dijital Da Na Kirkirarriyar Basira

July 31, 2025
Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”

Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”

July 31, 2025
Tinubu Ya Tsawaita Wa’adin Shugaban Kwastan Da Shekara Ɗaya

Tinubu Ya Tsawaita Wa’adin Shugaban Kwastan Da Shekara Ɗaya

July 31, 2025
Kare Ya Ciji Tsohon Ɗan Wasan Barcelona A Mazakuta

Kare Ya Ciji Tsohon Ɗan Wasan Barcelona A Mazakuta

July 31, 2025
An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina

July 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.