• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Janye ‘Yansandan Da Ke Aikin Kare Masu Hannu Da Shuni

by Leadership Hausa
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Kirsimeti: An Tsaurara Tsaro A Kwara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanan nan ne Karamar Ministar harkokin ‘Yansanda, Imaan Suleiman Ibrahim, ta sanar da umarnin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu na janye jami’an ‘yansanda da ke aikin kare masu hannu da shuni a fadin tarayyar kasar nan tare da sauya musu wurin aiki nan take ba tare da bata lokaci ba.

Ta kuma bayyana cewa, a cikin umarnin a kwai shirin samar da tsarin tabbatar da tsaro a unguwanni. Mun yi murnar samar da jami’an tsaro a cikin al’umma a matsayin mataki na yaki da masu aikata laifuka a sassan kasar nan.

  • Sanata Kaka Lawan Ya Gabatar Da Kudirin Tattara Dokokin Nijeriya Na Tsawon Shekara 19
  • Zaben Kano: ‘Yansanda Da Masu Zanga-zanga Sun Yi Arangama A Kano

Samar da tsaro ta hanyar amfani da al’umma yana daga cikin abubuwan da ake tattaunawa a tarukan jama’a na tsawon lokaci ana kuma ganinsa a matsayin wani mataki da zai kawo karshen matsalar tsaron da ake fuskanta wadda take dada karuwa a kullum musamman a yankunan karkara inda masu garkuwa da mutane da ‘yan bindiga ke gallaza wa al’umma.

Amma kafin mu koma ga irin wannan tsarin samar da tsaron bari mu koma a kan maganar yadda jami’an tsaro ke bayar da kariya ga masu hannu da shuni a cikin al’umma, lamarin da ya munana ta yadda duk wani mai kudi a aljihunsa kuma zai iya biya sai ya nemi ‘yansanda su rika ba shi kariya.

Wani tsohon shugaban hukumar kula da aikin ‘yansanda, kuma tsohon shugaban rundunar ‘yansandan Nijeriya, Mista Mike Okiro, ya yi gargadi a kan yadda wasu ‘yan kalilan da ya kwatanta da masu hannu da shuni da kuma wasu ‘yan kadan daga cikin al’umma suke amfani da jami’an ‘yansanda fiye da 150,000 don biyan bukatun kansu.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Ya kuma ce, kasar nan ba za ta iya daukar yadda kusan rabin jami’an rundunar ‘yansanda ke aiki a hannun wasu mutane masu zaman kansu ba. Ya kuma yi korafin cewa, rundunar ‘yansanda ta kasa aiwatar da dokar janye jami’an ‘yansanda daga hidimta wa masu hannu da shuni ne saboda rashin kudi. Abin da wannan ke nufi shi ne wannan umarnin na Shugaban Kasa Tinubu na baya-bayan nan ba wai sabo ba ne, an sha bayar da irin wannan umarnin a baya amma masu amfana da al’amarin sun kasa bari a aiwatar da dokar.

Amma kuma ba wani sirri ba ne cewa, matsalar rundunar ‘yansandan Nijeriya wata aba ce da za a kwatanta da sarkakiyar kasar gaba daya. Duk da cewa, babbar matsalar da rundunar ke fuskanta ta shafi kudin gudanar da aiki amma kuma suna fuskantar karancin ma’aikata da za su taimaka musu kare al’umma yadda ya kamata, lamarin samar masu da kudi yana da muhimmaci amma shin wai rashin kudi ne matsalar ‘yansanda ko cin hanci da rashawa?.

Idan za a iya tunawa da al’amarin tsohon shugaban rundunar ‘yansada Tafa Balogun, hukumar EFCC ta tabbatar da ya sace fiye da naira Biliyan 16 cikin kudaden gudanar da rundunar.

Rundunar ‘yansandan Nijeriya a matsayinta ta daya daga cikin rundunonin tsaron kasar nan ya kamata ta bayar da muhimmanci ga rigakafin aukuwa da kuma gano masu shirin aikata laifuka ba wai su bar jami’anta na aikin kare wasu kalilan masu hannun da shuni ba a cikin al’umma.

A matsayin rundunar na hukuma mai aikin tabbatar da doka da oda, an dora wa rundunar aikin kare rayuka da dukiyiyoyin al’umma Nijeriya a duk inda suke a fadin kasar nan. Suna kuma yin haka ne ta hanyar aikawa da jami’ansu da sauran kayan aiki wurare masu muhimmanci don kare su daga ayyuykan bata gari. Haka kuma yana daga cikin ayyukan ‘yansanda samar da tsaro ga manyan ma’aikatan gwamnati da kuma manyan mutane da ke aikin gwamnati. Wannan abin da za a iya fahimta ne don wadanda ake karewa za su samu tabbacin suna da kariya a yayin da suke gudanar da aikinsu na yi wa kasa hidima.

Al’umma sun damu da ganin abin da ya kamata ya zama alfarma sai gashi an lalata shi, inda a halin yanzu jam’ai fiye da 150,000 maza da mata ke aikin kare wasu ‘yan kalilan a gidaje da ofishoshinsu na aiki, to lalai wannan ba abin da za a amince da shi ba ne.

A ra’ayijnmu ya kamata a janye ‘yansanda daga aikin ba da tsaro ga mutane da ba jami’an gwamnati ba ne, kuma da sauran masu hannun da shuni ya kamata a rage yawan jami’an ‘yansanda da ke aiki da su. A wasu lokutan sai a tura ‘yansanda fiye da biyar don gadin jami’in gwamnati daya, to lallai wannan ba abin a amince da shi ba ne.

Ba zai yiwu kasa ta yi ta fama da karancin jami’an ‘yansanda ba amma wasu da dama daga cikin jami’anta na can suna aikin kare wasu masu hannu da shuni. Don fuskantar matsalolin tsaron da ake fama da su a kasa, muna kira ga gwamnati da ta gaggauta kamma aikin daukar karin jami’an ‘yansanda a kuma tabbatar da suna yi wa kasa aiki ne ba wasu tsiraru ba.

Haka kuma wannan jaridar ta yi imani da cewa, ya kamata a tabbatar da an samar wa rundunar ‘yansanda isassun kudi da kayan aiki na zamani in har ana son su yi aiki yadda ya kamata kamar yadda ‘yansanda ke aiki a wasu kasashen duniya da suka ci gaba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murna Ga Baje Kolin Cinikayyar Digital Na Kasa Da Kasa Karo Na Biyu

Next Post

Zargin Kafar Angulu Ga Dimokuradiyyar Nijeriya: Cacar Baki Ta Barke Tsakanin ‘Yan Adawa Da Gwamnati

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

22 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

2 days ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

2 days ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

2 days ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

2 days ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

3 days ago
Next Post
Zargin Kafar Angulu Ga Dimokuradiyyar Nijeriya: Cacar Baki Ta Barke Tsakanin ‘Yan Adawa Da Gwamnati

Zargin Kafar Angulu Ga Dimokuradiyyar Nijeriya: Cacar Baki Ta Barke Tsakanin 'Yan Adawa Da Gwamnati

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.