ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Janye ‘Yansandan Da Ke Aikin Kare Masu Hannu Da Shuni

by Leadership Hausa
3 years ago
Shuni

Kwanan nan ne Karamar Ministar harkokin ‘Yansanda, Imaan Suleiman Ibrahim, ta sanar da umarnin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu na janye jami’an ‘yansanda da ke aikin kare masu hannu da shuni a fadin tarayyar kasar nan tare da sauya musu wurin aiki nan take ba tare da bata lokaci ba.

Ta kuma bayyana cewa, a cikin umarnin a kwai shirin samar da tsarin tabbatar da tsaro a unguwanni. Mun yi murnar samar da jami’an tsaro a cikin al’umma a matsayin mataki na yaki da masu aikata laifuka a sassan kasar nan.

  • Sanata Kaka Lawan Ya Gabatar Da Kudirin Tattara Dokokin Nijeriya Na Tsawon Shekara 19
  • Zaben Kano: ‘Yansanda Da Masu Zanga-zanga Sun Yi Arangama A Kano

Samar da tsaro ta hanyar amfani da al’umma yana daga cikin abubuwan da ake tattaunawa a tarukan jama’a na tsawon lokaci ana kuma ganinsa a matsayin wani mataki da zai kawo karshen matsalar tsaron da ake fuskanta wadda take dada karuwa a kullum musamman a yankunan karkara inda masu garkuwa da mutane da ‘yan bindiga ke gallaza wa al’umma.

ADVERTISEMENT

Amma kafin mu koma ga irin wannan tsarin samar da tsaron bari mu koma a kan maganar yadda jami’an tsaro ke bayar da kariya ga masu hannu da shuni a cikin al’umma, lamarin da ya munana ta yadda duk wani mai kudi a aljihunsa kuma zai iya biya sai ya nemi ‘yansanda su rika ba shi kariya.

Wani tsohon shugaban hukumar kula da aikin ‘yansanda, kuma tsohon shugaban rundunar ‘yansandan Nijeriya, Mista Mike Okiro, ya yi gargadi a kan yadda wasu ‘yan kalilan da ya kwatanta da masu hannu da shuni da kuma wasu ‘yan kadan daga cikin al’umma suke amfani da jami’an ‘yansanda fiye da 150,000 don biyan bukatun kansu.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Ya kuma ce, kasar nan ba za ta iya daukar yadda kusan rabin jami’an rundunar ‘yansanda ke aiki a hannun wasu mutane masu zaman kansu ba. Ya kuma yi korafin cewa, rundunar ‘yansanda ta kasa aiwatar da dokar janye jami’an ‘yansanda daga hidimta wa masu hannu da shuni ne saboda rashin kudi. Abin da wannan ke nufi shi ne wannan umarnin na Shugaban Kasa Tinubu na baya-bayan nan ba wai sabo ba ne, an sha bayar da irin wannan umarnin a baya amma masu amfana da al’amarin sun kasa bari a aiwatar da dokar.

Amma kuma ba wani sirri ba ne cewa, matsalar rundunar ‘yansandan Nijeriya wata aba ce da za a kwatanta da sarkakiyar kasar gaba daya. Duk da cewa, babbar matsalar da rundunar ke fuskanta ta shafi kudin gudanar da aiki amma kuma suna fuskantar karancin ma’aikata da za su taimaka musu kare al’umma yadda ya kamata, lamarin samar masu da kudi yana da muhimmaci amma shin wai rashin kudi ne matsalar ‘yansanda ko cin hanci da rashawa?.

Idan za a iya tunawa da al’amarin tsohon shugaban rundunar ‘yansada Tafa Balogun, hukumar EFCC ta tabbatar da ya sace fiye da naira Biliyan 16 cikin kudaden gudanar da rundunar.

Rundunar ‘yansandan Nijeriya a matsayinta ta daya daga cikin rundunonin tsaron kasar nan ya kamata ta bayar da muhimmanci ga rigakafin aukuwa da kuma gano masu shirin aikata laifuka ba wai su bar jami’anta na aikin kare wasu kalilan masu hannun da shuni ba a cikin al’umma.

A matsayin rundunar na hukuma mai aikin tabbatar da doka da oda, an dora wa rundunar aikin kare rayuka da dukiyiyoyin al’umma Nijeriya a duk inda suke a fadin kasar nan. Suna kuma yin haka ne ta hanyar aikawa da jami’ansu da sauran kayan aiki wurare masu muhimmanci don kare su daga ayyuykan bata gari. Haka kuma yana daga cikin ayyukan ‘yansanda samar da tsaro ga manyan ma’aikatan gwamnati da kuma manyan mutane da ke aikin gwamnati. Wannan abin da za a iya fahimta ne don wadanda ake karewa za su samu tabbacin suna da kariya a yayin da suke gudanar da aikinsu na yi wa kasa hidima.

Al’umma sun damu da ganin abin da ya kamata ya zama alfarma sai gashi an lalata shi, inda a halin yanzu jam’ai fiye da 150,000 maza da mata ke aikin kare wasu ‘yan kalilan a gidaje da ofishoshinsu na aiki, to lalai wannan ba abin da za a amince da shi ba ne.

A ra’ayijnmu ya kamata a janye ‘yansanda daga aikin ba da tsaro ga mutane da ba jami’an gwamnati ba ne, kuma da sauran masu hannun da shuni ya kamata a rage yawan jami’an ‘yansanda da ke aiki da su. A wasu lokutan sai a tura ‘yansanda fiye da biyar don gadin jami’in gwamnati daya, to lallai wannan ba abin a amince da shi ba ne.

Ba zai yiwu kasa ta yi ta fama da karancin jami’an ‘yansanda ba amma wasu da dama daga cikin jami’anta na can suna aikin kare wasu masu hannu da shuni. Don fuskantar matsalolin tsaron da ake fama da su a kasa, muna kira ga gwamnati da ta gaggauta kamma aikin daukar karin jami’an ‘yansanda a kuma tabbatar da suna yi wa kasa aiki ne ba wasu tsiraru ba.

Haka kuma wannan jaridar ta yi imani da cewa, ya kamata a tabbatar da an samar wa rundunar ‘yansanda isassun kudi da kayan aiki na zamani in har ana son su yi aiki yadda ya kamata kamar yadda ‘yansanda ke aiki a wasu kasashen duniya da suka ci gaba.

Shuni
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
Next Post
Zargin Kafar Angulu Ga Dimokuradiyyar Nijeriya: Cacar Baki Ta Barke Tsakanin ‘Yan Adawa Da Gwamnati

Zargin Kafar Angulu Ga Dimokuradiyyar Nijeriya: Cacar Baki Ta Barke Tsakanin 'Yan Adawa Da Gwamnati

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.