• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Kawo Karshen Karancin Malaman Makarantun Firamare A Nijeriya

by Leadership Hausa
1 year ago
in Manyan Labarai
0
A Kawo Karshen Karancin Malaman Makarantun Firamare A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayanan da aka samu a rahoto na baya-bayan nan daga Hukumar Kula da Makarantun Firamare (UBEC) yana da matukar tayar da hankali. Rahoton shekarar 2022 zuwa 2023 na kididdigar yawan Malaman firamare da ake da su ya nuna cewa, Nijeriya na fuskantar karancin malamai a matakin firamare yayin da ake da gibin Malamai fiye da Malamai 195,000 a makarantun gwamnati na fadin tarayyar kasar nan.

Karancin kwararrun Malamai a matakin farko na tsarin ilimin kasar nan abu ne da ke bukatar a dauki matakin gaggawa daga dukkan matakan gwamnati da masu ruwa da tsaki a fadin kasar nan.

  • Bangaren Amurka Ya Mayar Wa Bangaren Sin Da Kayayyakin Tarihi 38 Da Suka Bata Daga Sin
  • Sharhi: Kokarin Fahimtar Yanayin Tattalin Arzikin Sin Ta Bangarorin Ayyuka Guda 3

Rahoton ya gano rashin daidatio a tsakanin sauran matakan ilimi, inda aka gano matakin makarantun reno na kananan yara da matakin karamar sakandare JSS suna da issasun Malamai har sun yi masu yawa amma kuma a matakin makarantun firamare suna matukar fuskantar matsalar rashin Malamai, a wasu kauyuka ma zaka ga Malami daya ne ko biyu ke aiki a dukkan makarantun da ake da su duk kuwa da yawan dalibai.

Wannan rashin daidaito na yawan Malamai a matakan ilimi na kasar nan shi ne ya jefa kasar cikin matsalolin da suke tattare da ilimin yara. Rahoton ya kuma bayyana cewa, rashin issasun Malamai a matakin firamari shi ne ya haifar matsalar talauci da sauran matsalolin da ake fuskata a Nijeriya.

A ra’ayin wannan jaridar,in har ba a samu kwararrun Malamai ba masu aiki tukuru tare da basu ingantaccen ilimi a bangaren makarantun firamare ta yaya za’a samu yara masu hazaka da za su zama abin alfaharinmu a nan gaba har su zama shugabannin gobe? Fatan kasar nan na tattare da magance wannan matsalar gaba daya.

Labarai Masu Nasaba

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

Abin takaici a nan shi ne abubuwan da suka haifar da wannan karancin Malamai a bayyane suke kuma kowa ya san su. Yawancin jihoji sun yi shekaru basu dauki sabbin Malamai ba, yayin da wasu ma’aikata ke barin aiki wasu kuma suna mutuwa amma ba a maye gurbinsu ba.

Wannan kuma na tattare da annobar barin kasa da aka fi sani da “japa” da kwararun Malamai ke yi, hakan ya sanya Malamai masu kwazo suna barin kasarnan zuwa kasashen waje don samun rayuwa ta gari abin da kuma shine ya kara haifar da matsalar da ake ciki.

Rashin kulawa da rashin kyawun ka’idojin aiki ga Malamai a Nijeriya yana kara taimakawa wajen korar kwararrun Malamai daga bangaren suna komawa wasu wuraren inda aka san mutuncin su.

Tuni shugaban kungiyar Malamai na kasa, NUT, Kwamrade Audu Titus Amba, ya nuna rashin jin dadinsa a kan lamariin, wannan kuma yana nuna irin kamarin da al’amarin ya kai ke nan.

Ya kuma bayyana cewa, ba za a iya samun ingantacen ilimi ba har sai an samu issasun Malamai a dukkan matakai na ilimi, musamman ma ganin ilimi shi ne kashin bayan ci gaban kowadanne al’umma.

Ba wai sun kasance a matsayin Malamai kawai ba ne, su masu saita yara ne tare da shiryar da su  domin su zama mutanen kirkin da za su zama shugabannin gobe.

Ba abin da za a amuince da shi ba ne a kasar da ke da yara fiye da  miliyan 12 da basu zuwa makaranta duk da kuma ana fuskantar tsananin rashin Malamai a matakin firamare.

Ta yaya za mu samar da ingantaccen ilimi da kuma rage yawan yaran da basu zuwa makaranta a Nijeriya bayan kuma muna fama da matsalar karancin malamai?

Lokacin daukar matakin da bai dace ba da daukar alkawurra marasa ma’ana ya wuce yanzu lokaci ne na daukar matakin da ya dace kai tsaye.

Abin jin dadin a nan shi ne, dama can a kwai daftarin tsarin farfado da tsarin ilimi a kasar nan, tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya kaddamar a shekarar 2020,an shirya daftarin ne don bunkasa tare da inganta sana’ar koyarwa a Nijeriya.

Wannan ya hada da samar da albashi na musamman ga Malaman firamare da na sakandare tare da kara shekarun barin aikin su hakanan kuma an samar da alawus alawsu ga dalibai masu koyon aikin Malanta don karfafa masu shiga harkar koyarwar.

Abin takaici a na shi ne irin wannan kyawawan matakai da kudurori ba a kai ga aiwatar da su ba har zuwa yanzu wanda hakan ke ci gaba da sanya harkar koyarwa cikin halin ni ‘yasu.

Dole ne a gaggauta daukar mataki kan wannan lamarin da gaggawa, sai aiwatar da abin da ke tatatare cikin shi rahoton.Muna kira da wannan gwammantin a karkashin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ta amince da daukar muhimmin mataki wajen aiwatar da tsare-tsaren da tsohon shugaban kasa Buhari ya yi na farfado da bangaren ilimi.

Bayan haka kuma dole gwamnatocin jihohi su dauki nasu alhakin.Dole su gaggauta fara daukar sabbin Malamai don cike gurbin Malaman firamare da aka rasa musamman a yankunan karkara.

Ya kuma kamata a kara inganta ka’idar aiki da jin dadin Malamai don aikin ya zama yana da ban sha’awa ta yadda kwarrarun Malamai za su tsaya a cikin aikin ba tare da shirin tserewa zuwa kasashen waje ba.

Lokaci ya yi da gwamnati tare da hadin gwiwar dukakan masu ruwa da tsaki  su dauki matakin ganin kowanne yaro a Nijeriya ya samu damar zuwa makarannta tare da samun ilimin da ya kamata.

Nasarar yaran Nijeriya dama nasarar Nijeriyar tana tattare ne da nasarar da aka samu a wannan kokarin. In muka zuba jarin da ya kamata a bangaren ilimi za mu samar da yaran da za mu yi alfahari da su a nan gaba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mutane Fiye Da Miliyan 141 Sun Shiga Ko Fita Daga Kasar Sin A Rubu’in Farko Na Bana

Next Post

Kasafin 2024 Ya Tona Asirin Yadda Ma’aikatu Ke ‘Sharholiya’

Related

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

6 hours ago
Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

12 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

14 hours ago
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja
Manyan Labarai

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

16 hours ago
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano
Manyan Labarai

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

18 hours ago
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba
Manyan Labarai

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

1 day ago
Next Post
Kasafin 2024 Ya Tona Asirin Yadda Ma’aikatu Ke ‘Sharholiya’

Kasafin 2024 Ya Tona Asirin Yadda Ma’aikatu Ke ‘Sharholiya’

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

September 15, 2025
Neja

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.