• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Nijeriya Ake Sarrafa Taliyar Indomie, Ana iya Amfani Da Ita Ba Matsala – Shugabar NAFDAC

by yahuzajere
2 years ago
in Labarai
0
A Nijeriya Ake Sarrafa Taliyar Indomie, Ana iya Amfani Da Ita Ba Matsala – Shugabar NAFDAC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An tunasar da ‘yan Nijeriya masu amfani da Taliyar Indomie da su sani cewa ana sarrafa ta ce a kasar nan ba wai ana shigo da ita daga kasar waje ba, haka kuma sinadaran da ake yin amfani da su wajen sarrafa ta na ethylene oxide ba a Nijeriya ake samar da shi ba.

Duk da cewa, Taliyar ta Instant Noodles, na daga cikin haramttauun kayan da aka haramta shigo da su cikin kasar nan, an shawarci masu yin amfani da wacce ake sarrafawa a Nijeriya da su saye ta su kuma yi amfani da ita.
Akwai fargaba ga wasu ‘yan Nijeriya ganin cewa ana magana a kan Taliyar ta instant Noodles a faɗin duniya a halin yanzu.

  • Shugabannin Da Aka Zaba Na Da Jan Aikin Hada Kan Nijeriya – Lawan

Da an yi maganar Taliyar ta noodles kawai ana ɗaukar Taliyar Indomie ake nufi.

Wannan na faruwa ne ganin cewa Indomie na a kan gaba a  kasuwar da ta yi a fadin duniya a fannin sarrafa noodles.

Hakazalika, wannan matsayin ya zo ne daidai lokacin da ake son inganta Taliyar da rabar da ita.

Labarai Masu Nasaba

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

A 2022, wani rahoto da aka fitar a kasuwar da ke a Gabashi da Kudancin Afirka da aka wallafa a kafar yanar Gizo wato (COMESA) an gargaɗi ‘yan Kasar Masar kan su guji cin  wasu nau’uka na Taliyar Indomie Instant Noodles saboda zargin tana dauke da wasu nasadarai da za su iya shafar kiwon lafiyarsu.

Kamar a yankin Larabawa, fargaba ta ci gaba da yaduwa a kasashen da ke makwabta da iyakokin Masar.

Hakazalika, a Nijeriya wasu kafafen yaɗa labara sun ci gaba da wallafa rahoton da ya fito daga Masa. Inda suka ci gaba da jefa tsoro a zukatan ‘yan Nijeriya, inda hakan ya sa Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta ƙasa NAFDAC da Hukumar kula da ingancin sarrafa kaya ta ƙasa (SON) suka shigo cikin lamarin tare da tsunduma kan yin aiki game da maganar guraɓatacciyar Taliyar da ake shigowa da ita cikin ƙasar nan ta hanyar fasa-ƙwaurin ta.

A ƙarshen bincike, an gano cewa, ba a saɓa ka’idar iyaka ba wajen shigo da ita kuma kasuwanninmu ba su fuskantar wata barazana.

An gano sanadarin na ethylene oxide a cikin Indomie na janyo cutar daji, a kasashen Taiwan, Malaysiya, inda bayanin da jami’an kiwon lafiyar kasashen suka yi ya haifar da raɗe-raɗi da jefa tsoro a cikin zukatan ‘yan Nijeriya.

 

Kafafen yada labara sun ci gaba da ƙara gishiri a miya tare da yin kanun labarai masu zafi don jefa fargaba a zukatan jama’a.

Kamfanin sarrafa taliyar ta Indomie a Taiwan da Malaysia da kuma kamfanin Dufil Prima Food Plc  da ke a Nijeriya  da ke sarrafa Indomie Instant Noodles a cikin kasar nan su ma an tantance su don guje wa kalubalen na cikin gida.

A hirarta da manema labarai, Darakta Janar ta NAFDAC, Mojisola Adeyeye ta sanar da cewa, Taliyar ta Instant noodles, na daga cikin kayan da gwamnatin tarayya ta haramta shigowa da su cikin kasar nan, inda ta ce, ita Taliyar da ake magana a kai hukumar ba ta yi mata rijista ba kuma sannan ba a Nijeriya ake sarrafa ta ba.

Ta ce muna yin takatsantsan don ganin ba a yi fasa-kwauarin ta zuwa cikin Nijeriya ba.

Shugaba sashen sadarwa da shirya tarurruka na kamfanin Dufil Prima Foods Plc, Tope Ashiwaju, ya bai wa ‘yan Nijeriya tabbacin cewa, ɗaukacin  nau’o’in Taliayarta Indomie Instant Noodles a cikin kasar nan ake sarrafa su kuma bisa doka da oda.

“Muna bin ƙa’idar inganci sau da ƙafa da Hukumar NAFDAC da Hukumar Kula da Ingancin Kayayyaki ta Ƙasa (SON) suka shimfiɗa a dukkan kamfanonin sarrafa kayanmu. Muna amfani ne kawai da kaya masu inganci da ake samarwa daga sahihan masu kawo kaya kuma ana duba na’urorin da muke aiki da su a kai a kai tare da tantance su domin tabbatar da cewa suna da ingancin da ya kamata.” In ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Nijeriya 376 Aka Kwaso Daga Sudan – Minista Sadiya

Next Post

An Sanya Sunan Pele Cikin Kamus A Brazil

Related

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita
Labarai

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

4 hours ago
NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

6 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

8 hours ago
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

9 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

11 hours ago
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Labarai

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

13 hours ago
Next Post
An Sanya Sunan Pele Cikin Kamus A Brazil

An Sanya Sunan Pele Cikin Kamus A Brazil

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.