• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Sake Fasalin Rundunar ‘Yansandan Nijeriya

by Leadership Hausa
1 year ago
in Ra'ayoyi
0
'yansanda
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kiran da ‘yan Nijeriya suka dade suna yi na neman a sake fasalin Rundunar ‘Yansanda kasar nan a halin yanzu ya zama wani lamari da ke bukatar a dauka da muhimmancin gaske. ‘Yan Nijeriya da dama sun yi ittifakin cewa, in har ana son Rundunar ‘Yansandan Nijeriya ta yi aikin kare al’umma da dukiyoyinsu yadda ya kamata dole a kakkabe duk wani burbushin mulkin mallaka da na sojoji da ke tattare da yadda suke gudanar da ayyukansu. Wadannan dabi’u ne suka sa ake yawan zarginsu da rashin iya aiki, cin hanci da kuma gallaza wa al’umma. A Nijeriya kamar sauran kasashe, an samar da rundunar ‘yansanda ne don kare al’umma tare da tabbatar da doka da oda amma ba wai don takura wa al’umma ba.

An dai fara samar da jami’an tsaron ‘yasanda a kasar nan ne a shekarar 1820, a zamanin mulkin mallaka, ta kuma fuskanci sauye-sauye da dama tun daga lokacin da aka kafa ta, amma kuma rundunar ta kasa tafiya daidai da zamani, ana kuma ganin yadda take gudanar da ayyukanta ba su dace da zamani ba. A kan haka ne, babu tantama in aka ce Rundunar ‘Yansandan Nijeriya na tsananin bukatar sauyin fasali don magance matsalolin da take fuskanta a kokarinta na karfafa wa al’umma gwiwa da kuma kokarinta na tabbatar da doka da oka a fadin tarayyar Nijeriya.

  • Gwamnatin Kano Ta Yi Kira A Kwantar Da Hankali Gabanin Hukuncin Kotun Daukaka Kara
  • Akwai Kyakkyawan Fata Game Da Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka A Wannan Karo

An sha yin kokarin ganin an sake fasalin rundunar a baya, amma al’amarin bai kai ga samun nasarar da ake bukata ba. Kokari na baya-bayan nan an yi shi ne bayan tarzomar da ta biyo bayan zanzangar #EndSARS da aka yi a watan Oktoba na shekarar 2020, yadda aka sake fasalin bai samar da sauyin da ake bukata ba, don bai yi maganin manyan matsalolin da ake fuskanta ba. A kan haka ne muke maraba da sabbin ‘yan kwamitin shugaban kasa a kan sauya fasalin Rundunar ‘Yansanda da aka kaddamar.

Kwamitin da ya hada da Ministan Harkokin ‘Yansanda, Ibrahim Geidam, mai ba shugaban kasa shawara a kan harkokin tsaron kasa, Nuhu Ribadu, Shugaban Hukumar Kula da Aikin ‘Yansanda, Solomon Arase da shugaban Kungiyar Gwamnonin Nijeriya kuma Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazak, an nemi su hada kai tare da samar da hanyoyin yi wa rundunar garambawul. Muna fatan a wannan karon gwamnati za ta gano bakin zaren warware matsalar yadda ya kamata.

A ra’ayinmu babban kalubalen da ke fuskantar Rundunar ‘Yansandan shi ne cin hanci da rashawa. Al’umma na ci gaba da kyamar ‘yansanda saboda yadda suka baci da cin hanci da rashawa a yayin gudanar da harkokinsu. Wannan ya haifar da rashin aminci a tsakanin ‘yansanda da al’umma, hakan na faruwa ne saboda ‘Yan Nijeriya na ganin kamar ‘yansanda sun fi damuwa ne da batun kudi a kan aikinsu na kare rayuka da dukiyoyin al’umma. Sakamakon wannan rashin aminci ne sau da dama al’umma ba su bayar da rahoton aikata laifuka a yankin da suke, saboda mutane na ganin babu wani amfani a taimakon ‘yansanda.

Labarai Masu Nasaba

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

Wani kalubalen da rundunar ‘yansandan ke fuskanta shi ne na yadda suka zama masu muzgunawa. An dade ana zargin ‘yansandan da amfani da karfin da ya wuce kima wajen gallaza wa ‘yan Nijeriya wanda yakan kai ga jin ciwo ko kuma mutuwa a wasu lokuta. Wannan yakan kai ga zanga-zangar neman a yi wa wanda aka kashe adalci amma sau da dama ba a yin komai don magance lamarin. An sha samun jami’an ‘yansanda sun kashe mutum amma babu wani mataki da ake dauka a kan jami’in da ya yi kisan.

Amma kuma muna tausaya wa ‘yansanda saboda za ka samu ba su da kayan aiki na zamai ba su kuma da horo na musamman na yadda za su gudanar da ayyukansu yadda ya kamata. ‘Yansanda da dama ba su da muhimman kayan aiki da suka hada da bindigogi, rigunan sulke da motocin sintiri. Wasu ma daga dan abin da ake ba su na albashi suke saya wa kansu tufafin aiki (uniform). Wannan na kawo musu cikas a yayin da aka nemi su kawo dauki na gaggawa don kare al’umma.

In har ana son ‘yansanda su gudanar da ayyukansu yadda ya kamata, dole sauyin fasalin da za a yi ya mayar da hankali wajen kawar da cin hanci da rashawa, kawo karshe cin zarafin al’umma da kuma magance rashin isassun kayan aiki a tsakanin ‘Yansandan Nijeriya, a kuma dawo da yarda da aminci a tsakaninsu da al’umma. Ya kuma kamata a samar musu da albashin da zai sa su kawar da kai daga karbar na goro daga al’umma, irin wanna ne yakan sa su nemi huce haushinsu a kan al’umma da zarar wani dan abu ya hada mutane da su.

Hanyar magance matsalar ita ce, dole gwamnati ta zuba jari wajen horas da jami’an ‘yansanda tare da samar musu da kayan aiki na zamani irin wanda ‘yansandan wasu manyan kasashen duniya ke amfani da su.

A bangaren ‘yansandan kuma, ya kamata a tabbatar da hukunta duk wani jami’n da aka samu da karbar cin hanci ko kuma wadanda suka ci zarafin mutane, a hukunta su kamar yadda doka ta tanada, wannan zai karfafa zuciyar al’umma ya kuma dawo da aminci a tsakanninsu da ‘yansandan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kayan Tarihi Na Manzon Allah (SAW)

Next Post

Wannan Kyauta Ce Ta Musamman Daga Daliban Makarantar Sakandaren Amurka

Related

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

2 months ago
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

6 months ago
Nijeriya
Ra'ayoyi

Ra’ayoyin ‘Yan Nijeriya A Kan Zagayowar Ranar Samun ‘Yancin Kai

7 months ago
Shekara 64 Da Samun ‘Yanci: Maimakon Biki, Jajantawa Ya Kamata A Yi – ‘Yan Nijeriya
Ra'ayoyi

Shekara 64 Da Samun ‘Yanci: Maimakon Biki, Jajantawa Ya Kamata A Yi – ‘Yan Nijeriya

7 months ago
Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
Ra'ayoyi

Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano

8 months ago
Dauda Lawal A Shekara 59: Mai Gidana Wanda Bai Da Jiji Da Kai
Ra'ayoyi

Dauda Lawal A Shekara 59: Mai Gidana Wanda Bai Da Jiji Da Kai

8 months ago
Next Post
Wannan Kyauta Ce Ta Musamman Daga Daliban Makarantar Sakandaren Amurka

Wannan Kyauta Ce Ta Musamman Daga Daliban Makarantar Sakandaren Amurka

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.