• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abba Gida-Gida Bai Cancanci Zama Gwamnan Kano Ba –APC

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Abba Gida-Gida Bai Cancanci Zama Gwamnan Kano Ba –APC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar APC a Jihar Kano ta shigar da kara a gaban kotun sauraren kararrakin zaben gwamnan Kano da ke zamanta a Miller road, tana kalubalantar nasarar zababben gwamnan Kano, Abba Kabiru Yusuf na jam’iyyar NNPP.

Wakilinmu ya ruwaito cewa an shigar da karar ne a gaban kotun ta hanyar rajista, a ranar 9 ga Afrilu, 2023.

  • Mutum 17 Sun Shiga Hannu Kan Zargin Garkuwa Da Mutane A Ekiti
  • NIS Ta Kaddamar Da Shirin ‘Guguwa’ Don Dakile Kwararar ‘Yan Ci-Rani A Ribas

APC ta sanar da kotun cewa sunan zababben gwamnan jihar, Abba Kabiru Yusuf baya cikin jerin rajistar NNPP da ke hannun INEC.

APC ta bayyana a cikin karar cewa kafin zaben gwamna da aka gudanar a ranar 18 ga Maris, 2023, dan takarar jam’iyyar NNPP ya gaza cika sharuddan zama mamba jam’iyyar, don haka ake zargin bai cancanci tsayawa takara a zaben gwamna a karkashin jam’iyyar NNPP ba.

Bugu da kari mai shigar da kara suna rokon kotu da ta rusa wa’adin zaben Abba.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

APC ta bukaci kotun da ta amince da adadin kuri’un da aka kada ba bisa ka’ida ba, don haka a yi la’akari da yadda aka cire adadin kuri’un da aka soke ba bisa ka’ida ba tare da ayyana zaben a matsayin ‘Inconclusive’.

Masu gabatar da kara, sun bukaci NNPP da dan takararta na gwamna da INEC wa’adin kwanaki 21 don amsa batutuwan da masu shigar da kara a kai.

A wani lamari makamancin haka, kotun ta bai wa jam’iyyar APC takardar bukatar duba kayan zaben gwamna, a wani bangare na ci gaba da shari’ar su da NNPP a gaban kotu.

Mai ba da shawara kan harkokin shari’a na jam’iyyar APC Jihar Kano, Abdul Adamu Fagge, ya tabbatar da cewa tawagar jam’iyyar APC ta fara duba kayayyakin zaben da aka yi amfani a kananan hukumomi 44 da ke fadin jihar.

A cewarsa aikin duba kayayyakin yana gudana cikin kwanciyar hankali tare da goyon bayan dukkan bangarorin da abin ya shafa.

Ya kuma bayyana kwarin gwiwarsa na cewa babu wata tangarda da ake sa ran za ta kawo cikas ga aikin, inda ya ce an ba su damar yin amfani da dukkan kayan ya zuwa yanzu, inda ya ce jam’iyyar za ta bibiyi lamarin har zuwa ga doka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCkanoKaraKotuNNPPZababben Gwamnan KanoZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mutum 17 Sun Shiga Hannu Kan Zargin Garkuwa Da Mutane A Ekiti

Next Post

Xi Jinping: Akwai Makoma Mai Haske A Fannin Raya Sana’o’i Na Musamman A Yankunan Karkara

Related

NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

3 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

5 hours ago
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

11 hours ago
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

12 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

15 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

1 day ago
Next Post
Xi Jinping: Akwai Makoma Mai Haske A Fannin Raya Sana’o’i Na Musamman A Yankunan Karkara

Xi Jinping: Akwai Makoma Mai Haske A Fannin Raya Sana’o’i Na Musamman A Yankunan Karkara

LABARAI MASU NASABA

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

September 18, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.