• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abdullahi Adamu: Babu Wani Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa Da Aka Haramta Wa Takara A APC

by yahuzajere
3 years ago
Abdullahi Adamu

Abdullahi Adamu

Abdullahi Adamu, shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, ya ce, babu wani ɗan takarar shugaban ƙasa da aka haramtawa tsayawa takara a zaɓen fidda gwani na jam’iyyar.

A ranar Juma’ar da ta gabata ne kwamitin tantancewa ƙarƙashin jagorancin John Oyegun, tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa ya gabatar da rahotonsa ga shugaban jam’iyyar APC.

Oyegun ya ce, kwamitin ya fito da jerin sunayen ’yan takara 13 daga cikin 23 da suka gabatar da kansu domin tantancewa.

  • Gwamnonin APC Suna Goyan Bayan Osinbajo A Zaben Fidda Gwani
  • ‘Yan Bindiga Sunyi Garkuwa Da Mahaifiyar A.A Zaura

Da ya ke magana da manema labarai a ranar Asabar, Adamu ya ce, tantancewar tamkar jarrabawa ce da ɗalibai ke fitowa da maki daban-daban.

Rahotanni sun nuna cewa, mutum 13 da ke fatan tsayawa takarar shugaban ƙasa an kasafta su cikin jerin sunayen waɗanda Oyegun ke jagoranta, yayin da sauran goman da ke fatan shugaban ƙasa ba su shiga cikin jerin sunayen ba.

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

Waɗanda aka sanya a cikin jerin sune Tinubu, mataimakin shugaban ƙasa Yemi Osinbajo; Rotimi Amaechi, ministan sufuri; Ahmad Lawan, shugaban majalisar dattawa; Yahaya Bello, gwamnan Kogi; Kayode Fayemi, gwamnan Ekiti, da Emeka Nwajiuba, tsohon ƙaramin ministan ilimi.

Sauran sun haɗa da Ogbonnaya Onu, tsohon ministan kimiyya da fasaha; Ibikunle Amosun, tsohon gwamnan Ogun; David Umahi, gwamnan Ebonyi, Muhammad Badaru, gwamnan Jigawa; Godswill Akpabio, tsohon gwamnan Akwa Ibom; da Tein Jack-Rich, wani ma’aikacin mai.

Sauran ’yan takara 10 da ba a sanya su cikin jerin ba sun haɗa da Tunde Bakare, Rochas Okorocha, Ben Ayade, Sani Yerima, Ken Nnamani, Ikeobasi Mokelu, Demeji Bankole, Felix Nicholas, Uju Ken-Ohanenye, da Ajayi Borroffice.

Abdullahi Adamu dai ya mike haikan wajen ganin APC ta tsayar da dan takarar da zai samu karbuwa a wurin ‘Yan Nijeriya domin jam’iyyarsa ta ci gaba da jan ragamar mulkin Nijeriya a 2023.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja
Labarai

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

November 7, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha
Siyasa

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump
Labarai

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Next Post
Zaben Fidda Gwani: An bukaci Deliget Din APC Da Su Zabi Osinbajo

Zaben Fidda Gwani: An bukaci Deliget Din APC Da Su Zabi Osinbajo

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

November 7, 2025
Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)

Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)

November 7, 2025
Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

November 7, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya

November 7, 2025
An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

November 7, 2025
Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

November 7, 2025
Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta

Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta

November 7, 2025
Xi Jinping Ya Taya Paul Biya Murnar Tazarce a Kamaru

Xi Jinping Ya Taya Paul Biya Murnar Tazarce a Kamaru

November 7, 2025
Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026

Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026

November 7, 2025
An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano

An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.