• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Manoman Doya A Jihar Edo Suke Kokawa

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Abin Da Ya Sa Manoman Doya A Jihar Edo Suke Kokawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Manoma sun koka akan rashin samun dauki a fannin noman amfanin gona da suka hada da, Rogo, Doya, Shibkafa da sauran amfanin gona.

Shugaban kungiyar manoman Doya na jihar Edo Luke Osagie ya bayyana hakan a hirarsa da manema labarai a jihar.

  • Yadda Wata Mata Ta Auri Kanta A Amurka
  • Shawarar Da Shugabar Cibiyar Kasuwanci Ta Duniya Ta Bai Wa Sabbin Gwamnoni

Sai dai, Osagie ya sanar da cewa, duk da irin wannan kalubalen da maoman Doyar ke fuskanta a jihar manoman ta a jihar na ci gaba da samun nasarori, musaman wajen samun girbi da dimbin riba mai yawa.

Shugaban ya  buga misali da yadda Fulani makiyaya ke shigar masu gonakansu, inda dabbibin su ke cinye masu amfanin gonakan su da suka noma.

“Duk da irin wannan kalubalen da maoman Doyar ke fuskanta a jihar manoman ta a jihar na ci gaba da samun nasarori, musaman wajen samun girbi da dimbin riba mai yawa.”

A cewarsa, akasari muna zama a cikin gonakan mu ko kuma ani jeji da ke a kusa da gonakan domin hana makiyayan shiga cikin gonakan namu.

Ya kara da cewa, idan muka hana su shiga cikin gonakan suna yin fada damu, inda mu kuma muke mayar masu da martani, wasu kuma makiyayan don gudun kar makiyayan su halaka su, suna arce wa su bar gonakan nasu.

“Akasari muna zama a cikin gonakan mu ko kuma ani jeji da ke a kusa da gonakan domin hana makiyayan shiga cikin gonakan namu.”

Shugaban ya kara da cewa, na biyu kuma gwamnatin jihar, ba ta bai wa noman Doyar mahimmancin da ya dace, har da sauran amfanin gona da manoman jihar suke noma wa tare da rashin samar mana da daukin da ya dace.

“Idan muka hana su shiga cikin gonakan suna yin fada damu, inda mu kuma muke mayar masu da martani, wasu kuma makiyayan don gudun kar makiyayan su halaka su, suna arce wa su bar gonakan nasu.”

“Gwamnatin jihar, ba ta bai wa noman Doyar mahimmancin da ya dace, har da sauran amfanin gona da manoman jihar suke noma wa tare da rashin samar mana da daukin da ya dace.”

A cewrsa, hakan ya janyo mutane a jihar, ba su da sha’awar yin noman na Doyar, inda ya bayyana cewa, ana samun dimbin riba a fannin na Noman Doya.

“Hakan ya janyo mutane a jihar, ba su da sha’awar yin noman na Doyar, inda ya bayyana cewa, ana samun dimbin riba a fannin na Noman Doya. ”

A wani labarain kuwa, Kwamishinan ma’aikatar aikin gona na Jihar Kebbi, Barista Attahiru Maccido ya ce, kashi 80 cikin 100 na manoman jihar kananan manoma ne da ke bukatar ilimin zamani domin inganta harkarsu ta noma.

Maccido ya bayyana haka ne lokacin da yake zantawa da a ofishinsa a Birnin Kebbi, inda ya shawarci manoman jihar su tashi tsaye wajen yin amfani da kayayyakin zamani domin inganta harkarsu ta noma.

Maccido ya ce noma hanya ce ta yin arziki inda wadansu jama’a suka dauke shi sana’ar wahala, inda ya ce, yanzu kasashen waje sun yi nisa wajen inganta sana’ar noma daga yadda ake yin sa a shekarun baya zuwa na zamani.

A cewarsa, ya zama wajibi manoma su tashi tsaye wajen inganta wannan sana’a tasu, da kuma su daukart fannin a matsayin sana’a domin ta haka ne za su rika bin duk hanyoyin da suka dace wajen inganta noman.

Kwamishina ya kara da cewa, Thailand ce da ta shahara wajen noman shinkafa da samar da abinci a duniya amma kuma abin mamaki, kasar ba ta da rabin kasar noma irin wadda Allah ya ba Nijeriya.

Ya sanar da cewa, saboda yin amfani da bincike da kimiyya yanzu Thailand tana kan gaba wajen samar da abinci ga kasashen duniya mu ma Jihar Kebbi haka muke son mu zama a kan gaba a cikin kasashen duniya masu alfahari da aikin noma.

Ya ce, tun ranar da Shugaba Muhammadu Buhari ya kaddamar da aikin noma a Jihar Kebbi aikin noma ya farfado saboda ko an mika ragamar aikin noma ga mai kishin kasa da son jama’a su zama masu dogaro da kansu domin samun karin arziki.

Kwamishinan ya ce, gwamnatin Jihar Kebbi tana kokari wajen taimaka wa manoman jihar da dabarun zamani da za su taimaka musu domin inganta noma a fadin jihar.

Ya ce, ko a kwanakin baya gwamnatin jihar ta rarraba wa manoma kudaden tallafin yin noman rani na shekara 2019.

Kwamishinan ya ci gaba da cewa, manoma 8,600 suka samu Naira bashin Naira dubu 150 kowanensu, inda ya kara da cewa, a shekara uku da suka gabata manoman shinkafa dubu 120  suka amfana da tallafin yin noma, sai manoman waken suya dubu biyar da suka amfana da shirin ba da tallafin noma, manoma alkama manoma dubu 1600 gwamnatin jihar ta ba rancen noman alkama.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DoyaEdoKokawaNoma
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamntin Tarayya Da Ta Ogun Sun Fara Yi Wa Dabbobi Allurar Riga-kafin Cuttutuka

Next Post

Dabi’ar Wasu Maza Ta Kiran ‘Yan Mata A Waya A Gaban Matansu

Related

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

1 week ago
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON
Noma Da Kiwo

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

1 week ago
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

3 weeks ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

3 weeks ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

4 weeks ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

4 weeks ago
Next Post
Dabi’ar Wasu Maza Ta Kiran ‘Yan Mata A Waya A Gaban Matansu

Dabi’ar Wasu Maza Ta Kiran ‘Yan Mata A Waya A Gaban Matansu

LABARAI MASU NASABA

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

September 14, 2025
Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

September 14, 2025
Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

September 14, 2025
Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

September 14, 2025
An Karrama Fitattun Fina-Finai A Bikin “Golden Panda” Da Ya Gudana A Lardin Sichuan Na Kasar Sin

An Karrama Fitattun Fina-Finai A Bikin “Golden Panda” Da Ya Gudana A Lardin Sichuan Na Kasar Sin

September 14, 2025
Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

September 14, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Wani Sojan Gona Ɗauke Da Bindiga A Katsina

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

September 14, 2025
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

September 14, 2025
Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.