ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Manoman Doya A Jihar Edo Suke Kokawa

by Abubakar Abba
3 years ago
Doya

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Manoma sun koka akan rashin samun dauki a fannin noman amfanin gona da suka hada da, Rogo, Doya, Shibkafa da sauran amfanin gona.

Shugaban kungiyar manoman Doya na jihar Edo Luke Osagie ya bayyana hakan a hirarsa da manema labarai a jihar.

  • Yadda Wata Mata Ta Auri Kanta A Amurka
  • Shawarar Da Shugabar Cibiyar Kasuwanci Ta Duniya Ta Bai Wa Sabbin Gwamnoni

Sai dai, Osagie ya sanar da cewa, duk da irin wannan kalubalen da maoman Doyar ke fuskanta a jihar manoman ta a jihar na ci gaba da samun nasarori, musaman wajen samun girbi da dimbin riba mai yawa.

Shugaban ya  buga misali da yadda Fulani makiyaya ke shigar masu gonakansu, inda dabbibin su ke cinye masu amfanin gonakan su da suka noma.

“Duk da irin wannan kalubalen da maoman Doyar ke fuskanta a jihar manoman ta a jihar na ci gaba da samun nasarori, musaman wajen samun girbi da dimbin riba mai yawa.”

A cewarsa, akasari muna zama a cikin gonakan mu ko kuma ani jeji da ke a kusa da gonakan domin hana makiyayan shiga cikin gonakan namu.

Ya kara da cewa, idan muka hana su shiga cikin gonakan suna yin fada damu, inda mu kuma muke mayar masu da martani, wasu kuma makiyayan don gudun kar makiyayan su halaka su, suna arce wa su bar gonakan nasu.

“Akasari muna zama a cikin gonakan mu ko kuma ani jeji da ke a kusa da gonakan domin hana makiyayan shiga cikin gonakan namu.”

Shugaban ya kara da cewa, na biyu kuma gwamnatin jihar, ba ta bai wa noman Doyar mahimmancin da ya dace, har da sauran amfanin gona da manoman jihar suke noma wa tare da rashin samar mana da daukin da ya dace.

“Idan muka hana su shiga cikin gonakan suna yin fada damu, inda mu kuma muke mayar masu da martani, wasu kuma makiyayan don gudun kar makiyayan su halaka su, suna arce wa su bar gonakan nasu.”

“Gwamnatin jihar, ba ta bai wa noman Doyar mahimmancin da ya dace, har da sauran amfanin gona da manoman jihar suke noma wa tare da rashin samar mana da daukin da ya dace.”

A cewrsa, hakan ya janyo mutane a jihar, ba su da sha’awar yin noman na Doyar, inda ya bayyana cewa, ana samun dimbin riba a fannin na Noman Doya.

“Hakan ya janyo mutane a jihar, ba su da sha’awar yin noman na Doyar, inda ya bayyana cewa, ana samun dimbin riba a fannin na Noman Doya. ”

A wani labarain kuwa, Kwamishinan ma’aikatar aikin gona na Jihar Kebbi, Barista Attahiru Maccido ya ce, kashi 80 cikin 100 na manoman jihar kananan manoma ne da ke bukatar ilimin zamani domin inganta harkarsu ta noma.

Maccido ya bayyana haka ne lokacin da yake zantawa da a ofishinsa a Birnin Kebbi, inda ya shawarci manoman jihar su tashi tsaye wajen yin amfani da kayayyakin zamani domin inganta harkarsu ta noma.

Maccido ya ce noma hanya ce ta yin arziki inda wadansu jama’a suka dauke shi sana’ar wahala, inda ya ce, yanzu kasashen waje sun yi nisa wajen inganta sana’ar noma daga yadda ake yin sa a shekarun baya zuwa na zamani.

A cewarsa, ya zama wajibi manoma su tashi tsaye wajen inganta wannan sana’a tasu, da kuma su daukart fannin a matsayin sana’a domin ta haka ne za su rika bin duk hanyoyin da suka dace wajen inganta noman.

Kwamishina ya kara da cewa, Thailand ce da ta shahara wajen noman shinkafa da samar da abinci a duniya amma kuma abin mamaki, kasar ba ta da rabin kasar noma irin wadda Allah ya ba Nijeriya.

Ya sanar da cewa, saboda yin amfani da bincike da kimiyya yanzu Thailand tana kan gaba wajen samar da abinci ga kasashen duniya mu ma Jihar Kebbi haka muke son mu zama a kan gaba a cikin kasashen duniya masu alfahari da aikin noma.

Ya ce, tun ranar da Shugaba Muhammadu Buhari ya kaddamar da aikin noma a Jihar Kebbi aikin noma ya farfado saboda ko an mika ragamar aikin noma ga mai kishin kasa da son jama’a su zama masu dogaro da kansu domin samun karin arziki.

Kwamishinan ya ce, gwamnatin Jihar Kebbi tana kokari wajen taimaka wa manoman jihar da dabarun zamani da za su taimaka musu domin inganta noma a fadin jihar.

Ya ce, ko a kwanakin baya gwamnatin jihar ta rarraba wa manoma kudaden tallafin yin noman rani na shekara 2019.

Kwamishinan ya ci gaba da cewa, manoma 8,600 suka samu Naira bashin Naira dubu 150 kowanensu, inda ya kara da cewa, a shekara uku da suka gabata manoman shinkafa dubu 120  suka amfana da tallafin yin noma, sai manoman waken suya dubu biyar da suka amfana da shirin ba da tallafin noma, manoma alkama manoma dubu 1600 gwamnatin jihar ta ba rancen noman alkama.

Doya
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Dabi’ar Wasu Maza Ta Kiran ‘Yan Mata A Waya A Gaban Matansu

Dabi’ar Wasu Maza Ta Kiran ‘Yan Mata A Waya A Gaban Matansu

LABARAI MASU NASABA

NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.