• English
  • Business News
Tuesday, October 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Muka Sa Takin Zamani Cikin Tallafin Jama’a – Gwamnan Filato

byAbubakar Abba
2 years ago
Takin zamani

Gwamnan Jihar Filato, Caleb Mutfwang ya bayyana cewa, gwamnatinsa ta sayo takin zamani da aka dauko a cikin manyan motoci sama da 200, domin raba wa al’ummar jihar a matsayin daya daga cikin matakan bayar da tallafi.

Mutfwang ya bayyana hakan ne a garin Jos; babban birnin jihar a lokacin da ya kai ziyarar aiki, domin duba takin zamani da ke tashar jiragen sojin sama a garin na Jos.

  • Cutar Anthrax: Yadda Masu Kiwon Dobbobi Suka Shiga Zullumi A Jos
  • Gidauniyar TY Buratai Ta Nemi ‘Yan Nijeriya Su Kara Hakuri Da Salon Mulkin Tinubu

Gwamnan ya ci gaba da cewa, babbar manufar samar da takin shi ne, domin samar da dauki tare da amfanin gona, musamman don a kara samar da wadataccen abinci a Jihar Filato da kuma matikin kasa baki-daya.

Bugu da kari ya bayyana cewa, kyakkyawan shiri na nan tafe ta yadda za a raba wannan taki na zamani, domin tabbatar da ganin ya isa ga wadanda ake so su amfana kai tsaye.
A cewarsa, “Muna so mu sanar da cewa, tuni mun bayar da umarnin shigo da manyan motoci 200 na takin zamani, wadanda a halin yanzu tuni an riga an dauko su”, in ji shi.

Gwamnan ya kara da cewa, muna kammala shirye-shiryen rabar da takin, za mu tura shi zuwa ga kananan hukumomi 17 na jihar.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

Kazalika gwamna Mutfwang ya bayyana muhimmancin yin amfani da takin wajen yin noma, amma ba kuma wai domin wadanda ake so su amfana da shi su karkata akalarsa wajen sayar da shi, don biya bukatun kashin kansu ba.

Sannan gwamnan ya kuma jaddada kokarin da gwamnatinsa ke yi na kara bunkasa fannin aikin noma a jihar ta Filato, musamman domin bai wa fannin taimakon da ya kamata domin amfanin al’umma baki-daya.

A nasa jawabin, Babban Sakataren Bayar da Agajin Gaggawa na Jihar Filato (PLASEMA), Hon. Sunday Abdu ya sanar da cewa, sama da manyan motoci 170 dauke da takin zamani aka sauke tare da jiran karin wasu manyan motoci 40 nan gaba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

October 3, 2025
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

October 3, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

September 27, 2025
Next Post
Messi

Messi Zai Iya Lashe Kyautar Ballon D'or Ta Bana

LABARAI MASU NASABA

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Na Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Korea Ta Arewa

Firaministan Sin Zai Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Na Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Korea Ta Arewa

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version