• Leadership Hausa
Saturday, December 9, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cutar Anthrax: Yadda Masu Kiwon Dobbobi Suka Shiga Zullumi A Jos

by Sulaiman
4 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Cutar Anthrax: Yadda Masu Kiwon Dobbobi Suka Shiga Zullumi A Jos
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Makiyaya a garin Jos da ke Jihar Filato, na ci gaba da nuna damuwarsu biyo bayan gano bullar cutar da ke harbin dabbobi (Anthrax) daga Jihar Neja.

“Akwai bukatar daukan matakan gaggawa yadda ya kamata domin dakile yaduwar cutar zuwa wannan gari namu na Jos.”
Haka zalika, Ma’aikatar aikin noma da raya karkara ta tarayya ce ta sanar da bullar wannan cuta da aka gano a Jihar ta Neja a makon da ya gabata, inda gano bullar cutar ya sanya makiyayan na garin Jos shiga matukar tashin hankali.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Ja Hankulan Jama’a Kan Barkewar Cutar Anthrax A Ghana

Harwa yau, a ranar 14 ga watan Yulin 2023 ne Ofishin babban likitan dabbobi na kasa ya tabbatar da gano alamomin wannan cuta (Anthrax), a wata gona da ke Karamar Hukumar Suleja Jihar Nejan.

Wannan gona da ke garin Gajiri, daura da babban titin Abuja zuwa Kaduna a Karamar Hukumar Suleja, na dauke da rukunin dabbobi iri daban-daban da suka hada da Shanu, Akuyoyi da sauran makamantan su.
Biyo bayan bullar cutar a wannan gona ne, ya sanya wasu daga cikin makiyaya da sauran masu kiwo a garin na Jos shiga dimuwa da furgici tare da yin kiraye-kiraye don ganin an dakile ci gaba da yaduwarta.

“Ina da masaniya kwarai da gaske a kan wannan cuta, sannan ko shakka babu ina cikin matukar damuwa tun daga lokacin da na samu labarin tabbacin bullar ta a Jihar Neja,” a cewar wani makiyayi a Jos, Muhammad Rabi’u.

Labarai Masu Nasaba

Kurakuran Da Wasu Ke Tafkawa A Noma Don Kasuwanci

Manoman Karkara Sun Nuna Farin Ciki Da Yadda Suka Amfana Da Tallafin IFAD

Muhammad ya ci gaba da cewa,“ ina kiwon shanu da tumaki, sannan a garken nasu nake kwana. Don haka, wajibi ne na kasance cikin firgici da damuwa.”
Daga nan ne, sai ya yi kira ga Gwamnatin Jihar Filo da ta gaggauta daukar matakan da suka dace domin dakile yaduwar a fadin jihar baki-daya.

Shi ma wani makiyayin mai suna Babangida Musa ya bayyana nasa ra’ayin cewa, tun fil azal akwai wannan cutar, ba wai yanzu ba ne ta fara bayyana, sai dai kawai a kara tsaurara bincike tare da kokarin ganin an magance ta, ba ma a garin na Jos kadai ba, har ma fadin kasa baki-daya.

“Muna iya bakin kokarinmu na ganin wannan cuta ba ta ci gaba da yaduwa a wannan gari namu na Jos ba, sannan muna kuma yin kira ga Gwamnatin Jihar Filato, don sake ci gaba da dage damtse wajen daukar matan gaggawar day a kamata domin dakile yaduwar ta,” in ji Babangida.

Kazalika, wani makiyayin daga Jihar Neja mai suna Malam Muhammad ya karkare da cewa, “Bayan samun labarin bullar alamomin wannan cuta a Jihamu ta Neja, mun yi matukar kaduwar tare da shiga razani. Don haka, muke kira ga gwamnati da babbar murya don dakile ci gaba da yaduwar cutar a sauran gurare daban-daban.”

“Muna rokon Gwamnatin Jihar ta Filato da ta dakile yaduwar cutar zuwa cikin jihar, musamman ma cikin garin Jos da kewayensa. Muna kuma addu’ar kada cutar ta ci gaba da yaduwa sauran jihohin da ke a fadin wannan kasa,” in ji shi.

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hambararriyar Gwamnatin Bazoum Ta Nemi Faransa Ta Kwace Mulki Daga Sojojin Nijar

Next Post

Yadda Ake Sarrafa Rubutu Ta Word-Processing

Related

NOMA
Noma Da Kiwo

Kurakuran Da Wasu Ke Tafkawa A Noma Don Kasuwanci

2 hours ago
IFAD
Noma Da Kiwo

Manoman Karkara Sun Nuna Farin Ciki Da Yadda Suka Amfana Da Tallafin IFAD

3 hours ago
Masu Sarrafa Waken Soya Na Neman A Haramta Fitar Da Shi Waje
Noma Da Kiwo

Masu Sarrafa Waken Soya Na Neman A Haramta Fitar Da Shi Waje

6 days ago
Nijeriya Na Fuskantar Karancin Kayan Noma
Noma Da Kiwo

Nijeriya Na Fuskantar Karancin Kayan Noma

1 week ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Noman Rani A Jihar Neja
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Noman Rani A Jihar Neja

2 weeks ago
Hanyoyin Warware Kalubalen Da Kiwon Kifi Ke Fuskanta A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Hanyoyin Warware Kalubalen Da Kiwon Kifi Ke Fuskanta A Nijeriya

2 weeks ago
Next Post
Yadda Ake Sarrafa Rubutu Ta Word-Processing

Yadda Ake Sarrafa Rubutu Ta Word-Processing

LABARAI MASU NASABA

COP28: Sin Da Afirka Za Su Bunkasa Hadin Gwiwa A Fannin Raya Kananan Ayyukan Samar Da Makamashi Mai Tsafta

COP28: Sin Da Afirka Za Su Bunkasa Hadin Gwiwa A Fannin Raya Kananan Ayyukan Samar Da Makamashi Mai Tsafta

December 9, 2023
NOMA

Kurakuran Da Wasu Ke Tafkawa A Noma Don Kasuwanci

December 9, 2023
Ministan Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Mali

Ministan Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Mali

December 9, 2023
IFAD

Manoman Karkara Sun Nuna Farin Ciki Da Yadda Suka Amfana Da Tallafin IFAD

December 9, 2023
NPA

NPA Ta Bayyana Dalilan Dawo Da Kwangilar Kamfanin INTELS

December 9, 2023
Nijeriya

Kayan Da Nijeriya Ke Fitarwa Waje Sun Karu Zuwa Naira Tiriliyan 10.35

December 9, 2023
harkokin zabe

Amfani Da Fahasa Zai Bunkasa Harkokin Zabe –Agu

December 9, 2023
TGI

TGI Group Za Ta Hada Kai Da ABU Domin Bunkasa Kirkire-kirkire

December 9, 2023
Tinubu

Tinubu Zai Sake Fuskantar Wata Shari’ar A Kotun Koli Kan Zaben 2023

December 9, 2023
Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Za Ta Zaftare Kudaden Kananan Hukumomin Da Ba A Yi Zabe Ba

December 9, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.