ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cutar Anthrax: Yadda Masu Kiwon Dobbobi Suka Shiga Zullumi A Jos

by Sulaiman
3 years ago
Anthrax

Makiyaya a garin Jos da ke Jihar Filato, na ci gaba da nuna damuwarsu biyo bayan gano bullar cutar da ke harbin dabbobi (Anthrax) daga Jihar Neja.

“Akwai bukatar daukan matakan gaggawa yadda ya kamata domin dakile yaduwar cutar zuwa wannan gari namu na Jos.”
Haka zalika, Ma’aikatar aikin noma da raya karkara ta tarayya ce ta sanar da bullar wannan cuta da aka gano a Jihar ta Neja a makon da ya gabata, inda gano bullar cutar ya sanya makiyayan na garin Jos shiga matukar tashin hankali.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Ja Hankulan Jama’a Kan Barkewar Cutar Anthrax A Ghana

Harwa yau, a ranar 14 ga watan Yulin 2023 ne Ofishin babban likitan dabbobi na kasa ya tabbatar da gano alamomin wannan cuta (Anthrax), a wata gona da ke Karamar Hukumar Suleja Jihar Nejan.

ADVERTISEMENT

Wannan gona da ke garin Gajiri, daura da babban titin Abuja zuwa Kaduna a Karamar Hukumar Suleja, na dauke da rukunin dabbobi iri daban-daban da suka hada da Shanu, Akuyoyi da sauran makamantan su.
Biyo bayan bullar cutar a wannan gona ne, ya sanya wasu daga cikin makiyaya da sauran masu kiwo a garin na Jos shiga dimuwa da furgici tare da yin kiraye-kiraye don ganin an dakile ci gaba da yaduwarta.

“Ina da masaniya kwarai da gaske a kan wannan cuta, sannan ko shakka babu ina cikin matukar damuwa tun daga lokacin da na samu labarin tabbacin bullar ta a Jihar Neja,” a cewar wani makiyayi a Jos, Muhammad Rabi’u.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Muhammad ya ci gaba da cewa,“ ina kiwon shanu da tumaki, sannan a garken nasu nake kwana. Don haka, wajibi ne na kasance cikin firgici da damuwa.”
Daga nan ne, sai ya yi kira ga Gwamnatin Jihar Filo da ta gaggauta daukar matakan da suka dace domin dakile yaduwar a fadin jihar baki-daya.

Shi ma wani makiyayin mai suna Babangida Musa ya bayyana nasa ra’ayin cewa, tun fil azal akwai wannan cutar, ba wai yanzu ba ne ta fara bayyana, sai dai kawai a kara tsaurara bincike tare da kokarin ganin an magance ta, ba ma a garin na Jos kadai ba, har ma fadin kasa baki-daya.

“Muna iya bakin kokarinmu na ganin wannan cuta ba ta ci gaba da yaduwa a wannan gari namu na Jos ba, sannan muna kuma yin kira ga Gwamnatin Jihar Filato, don sake ci gaba da dage damtse wajen daukar matan gaggawar day a kamata domin dakile yaduwar ta,” in ji Babangida.

Kazalika, wani makiyayin daga Jihar Neja mai suna Malam Muhammad ya karkare da cewa, “Bayan samun labarin bullar alamomin wannan cuta a Jihamu ta Neja, mun yi matukar kaduwar tare da shiga razani. Don haka, muke kira ga gwamnati da babbar murya don dakile ci gaba da yaduwar cutar a sauran gurare daban-daban.”

“Muna rokon Gwamnatin Jihar ta Filato da ta dakile yaduwar cutar zuwa cikin jihar, musamman ma cikin garin Jos da kewayensa. Muna kuma addu’ar kada cutar ta ci gaba da yaduwa sauran jihohin da ke a fadin wannan kasa,” in ji shi.

Anthrax
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Yadda Ake Sarrafa Rubutu Ta Word-Processing

Yadda Ake Sarrafa Rubutu Ta Word-Processing

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.