Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

Abinda Aka Yi Wa ‘Yan Kwankwasiyya A Kano Alamun Nasara Ne – Nasir Isah

by Tayo Adelaja
September 6, 2017
in RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Shugaban Kungiyar Matasan Kwankwasiyya na Kasa (Kwankwasiyya National Youth Congress, KNYC), Nasir Isah Garun Malam, ya bayyana cewar abubuwan da suka faru game da harin da aka kai wa mabiyar darikar siyasar Kwankwasiyya yayin Hawan Daushe a Birnin Kano, alamu ne da suke nuna gazawar gwamnati mai ci a fili. A cewarsa, duk wani mutum da ya san tsarin siyasar ci gaban al’umma, bai za goyi bayan irin wannan sare-sare da sunan bambancin siyasa ba.

Nasir Garun Malam ya fadi haka ne a wani taron manema labarai da Kungiyar ta shirya a Birnin Abuja, inda ya ce sam abubuwan da suka faru sun sabawa tsarin siyasar ci gaban kasa da al’ummarta.

samndaads

Ya ce, hakika su ‘yan Kwankwasiyya ba su ji dadin abinda ya faru ba, kuma hakan alamun nasara ne ga tafiyarsu ta Kwankwasiyya, a cewarsa magoya bayan Gandujiyya sun kara haskawa duniya cewar ba za su iya tabuka wani abu a siyasance ba sai ta hanyar sara da suka.

“Wadanda suka aikata wannan abu sam ba ‘yan siyasa ba ne, ‘yan jagaliya ne kawai. Wadanda suke fushi da fushin wani. A matsayin Jihar Kano na alkiblar siyasar Nijeriya, bai dace irin wadannan abubuwa su rika faruwa ba.” In ji shi.

“Shugabanninmu da wannan abu ya rutsa da su masu hankali ne, shi ya sa ba su yi wata magana a kai ba, wanda na tabbatar su tsagin wadanda suka yi wannan abu ba haka suka so. Bukatarsu a yi kare-jini-biri-jini. Sai suka yi rashin sa’a, tuni Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya gama zuba madarar hankali a kwakwalen matasan Jihar Kano musamman mabiya Kwankwasiyya.

Ya ce, karon farko kenan a tarihin siyasa da irin haka ta taba faruwa, inda wasu gungun jama’a da suke ikirarin goyon bayan Gwamnati, za su dauki makami su rufarwa wani bangaren na ‘ya’yan jam’iyyar da suka yi sanadin hayewar jagoransu kan karagar mulki, ciki da har tsohon Sakataren Gwamnati da kuma kani ga tsohon Gwamna Rabiu Musa Kwankwaso.

“A tarihin Kano, Kwankwaso ne Gwamna na farko da ya hana daba ta hanyar yin amfani da ilmi; ya samarwa da matasa ayyukan a fanni daban-daban, wadanda ko makiyinsa ya sani. Matasa sun shagaltu da ayyukan ci gaba a wancan lokaci, saboda haka babu mai tunanin daukar makami ya farwa wani da sunan siyasa.

Nasir Isah ya kuma yi kira ga matasa da su daina bari ana amfani da su wajen jagaliyanci, domin a karshe babu wanda zai cutu sai su.

A karshe ya yi wa wadanda balahirar ta shafa addu’ar samun sauki tare da jinjina gare su bisa juriyarsu da suka na rashin mayar da martini. Inda ya ce lokaci na zuwa wanda mabiya darikar Kwankwasiyya za su rama a akwatunan zabe.

SendShareTweetShare
Previous Post

Ba Na Tsoron Buhari Ya Kore Ni Daga Aiki – Ministar Mata

Next Post

Farfadowar Tattalin Arzikin Nijeriya Shi Ne Talaka Ya Iya Cin Abinci Sau Uku A Rana- Atiku

RelatedPosts

Makiyaya Ondo

Korar Makiyaya A Ondo: Cikakken Rahoton Yadda Ta Kaya Taron Gwamnoni Da Shugabannin Fulani

by Muhammad
15 hours ago
0

Daga Khalid Idris Doya, Gwamnonin Nijeriya sun kira taron gaggawa...

Kasafin 2021

Hotunan Sabbin Shugabannin Rundunonin Tsaro

by Sulaiman Ibrahim
1 day ago
0

Major-Gen. Leo Irabor, Chief of Defence...

Garban

Garban Kauye Farawa Ne Allurar Dinke Barakar Kumbotso – Muslihu Yusuf Ali

by Muhammad
3 days ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, An bayyana zaben Sabon shugaban Karamar...

Next Post

Farfadowar Tattalin Arzikin Nijeriya Shi Ne Talaka Ya Iya Cin Abinci Sau Uku A Rana- Atiku

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version