ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ibtila’in Mutuwar Almajirai A Kebbi…

by Umar Faruk
2 years ago
kebbi
  • Sai Da Suka Shafe Minti 30 A Binne Kafin Kawo Musu Dauki
  • Halin Da Muka Tsinci Kanmu A Ciki – Malamin Almajiran
  • Jama’a Na Ci Gaba Da Tururuwar Shaida Lamarin
  • Tambayoyin Da Mutane Ke Yi Ga Gwamnatin Kebbi

Al’ummar Jihar Kebbi har ma da sauran sassan Nijeriya sun shiga alhini bayan rasuwar wasu almajirai takwas sakamakon wani dutse da ya yanke ya fado kan almajiran na Makarantar Allon Malam Dan Umma da ke Unguwar Badariya, cikin Karamar Hukumar Birnin Kebbi.

A safiyar ranar Asabar 20 ga watan Afrilun 2024, da misalin karfe 8 na safe ne iftila’in ya auku. Masana sun bayyana cewa tarihi ya nuna akalla dutsen ya kai kimanin shekaru 80 zuwa 100 da fitowa inda yake ta girma har ya mamaye waje mai yawan gaske.

  • Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Fitar Da Miliyan 309.5 Don Tallafawa Ɗaliban Da Ke Karatu a Ƙasashen waje 
  • Jami’an Tsaro sun Ceto Mata Biyu da aka Yi Garkuwa da Su A Kebbi

Haka kuma sun kara da cewa a lokacin da ba a fara amfani da kasar siminti ba sosai a yankin, jama’a da dama suna amfani da burbushin dutsen ne da kasar da yake cakude da shi wajen gina gidaje. Daga baya kuma dutsen ya koma filayen jama’a har ma da yawa sun gina gidajen kwana ta yadda a halin yanzu gidaje ne a ko ina a yankin da hatsarin ya auku.

ADVERTISEMENT

Saboda wannan al’ada ta amfani da kasar dutsen ne, almajiran da suka je hako kasa bisa umarnin malaminsu domin su gyara wasu ramuka da ke dakunansu, suna kan aiki kwatsam dutsen ya yanke ya taushe akalla su 10, inda nan take takwas suka riga mu gidan gaskiya, biyu suka tsira tare da garzayawa da su asibitin tunawa da Sarki Yahaya. Sai dai daga baya daya shi ma ya rasu, zuwa lokacin hada wannan rahoto almajiri daya ne ke jinya.

Rahotanni sun nunar da cewa wadanda hatsarin ya rutsa da su sun kai kimanin minti 30 a binne kafin a kawo musu agajin gaggawa daga jama’ar da ke unguwar.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Almajiran da suka rasa rayukansu a nan take da suka hada da Muhammad Bawada, Musa Kambaza, Dan Sayyada Kambaza, Nasiru Cheberu, dukkansu sun fito ne daga Karamar Hukumar Gwandu, sai kuma Yakubu da Aminu da sauransu da suka fito daga wurare daban-daban. Dukkan almajiran da suka rasa rayukansu babu wanda ya kai shekara 20 da haihuwa.

Binciken wakilinmu ya gano cewa wannan shi ne hatsari na farkon a tahirin fitowar dutsen duk da cewa mafi yawan gidajen jama’ar Unguwar Badariya da kewaye duk da kasar dutsen ne aka gina su amma ba a sumu irin wannan ba sai a kan wadannan almajiran.

Da yake tsokaci kan lamarin, malamin almajiran, Malam Dan Umma ya tabbatar da mutuwar almajiran takwas nan take, kana ya kara da cewa, “Yau daya ce daga cikin ranaku mafi bakin ciki a rayuwata. Abin da ya faru shi ne, na ba su umarnin cewa su je su gino kasar don gyara ramukan da ke cikin dakunansu saboda ruwan damina na zuwa. Daga nan sai suka tafi bakin dutsen da ke kusa da makarantar.

“Bayan mintoti kafin dawowarsu, sai wasu daga cikin almajiran suka sheko da gudu suna wayyo, wayyo, dutse ya taushe almajirai da suke ginar kasar a cikin dutsen. A nan take na garzaya wurin da lamarin ya faru, inda na tabbatar da mutuwarsu yayin da biyu da suka tsira kuma aka garzaya da su asibiti don tabbatarwa ko akasin hakan.”

Malam Dan Umma ya ci gaba da cewa, an ajiye gawarwakin almajiran da suka rasu a dakin ajiyar gawa na asibitin tunawa da Sarki Yahaya da ke Birnin Kebbi, kafin a kai su gidajen iyayensu domin yi musu jana’iza.
Bayan faruwar lamarin jama’ar unguwar Badariya da ma na cikin garin Birnin Kebbina ci gaba da tattaki zuwa bakin dutsen don gane wa idanunsu irin yadda lamarin ya faru.

Wasu da suka zanta da wakilinmu, sun bayyana ra’ayin cewa bai kamata a ce malamin almajiran ya ba su umarnin su je su hako kasar gyaran dakunansu ba, saboda kananan yara ne kuma wajen da suke kwana mallakin malamin don haka shi ya kamata ya gyara ba almajiran ba.

Sun kara da fadin cewa idan damina ta kankama, ruwa na gaggarowa daga dutsen zuwa cikin gidajen mutane saboda wasu gidajen a bisa hanyar ruwan daminar aka gina su. Ta hakan ne ake yawan samun matsalolin ambaliya da ke lakume rayukkan jama’a da kuma rasa matsuguni wanda sai sun nemi agajin gaggawa daga gwamnati da kuma wasu hukumomi masu ba da agajin gaggawa idan aka samu ambaliyar ruwan sama.

Wakazalika, abin da mutane ke kara tambaya a kai shi ne, mutanen da ke zama kusa da dutsen sun samu izinin haka kuwa sannan hukumar kula da filaye da ta bunkasa birane sun yi la’akari da irin hadurran da ke tattare da zama a wannan wurin kuwa?

A halin yanzu dai jama’a sun zura ido su ga wane irin mataki ne Gwamnatin Jihar Kebbi za ta dauka domin riga-kafin lamarin a gaba.

kebbi
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnatin Kebbi Ta Amince Da ₦2.07bn Alawus-alawus Ga Ma’aikatan Manyan Makarantu
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Maye Gurbin Mataimakinsa Da Ibrahim Augie A Zaɓen 2027
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Matashi Ya Shiga Hannu Kan Zargin Wulaƙanta Alƙur’ani A Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Miƙa Yara 5 Da Aka Ceto Daga Hannun Masu Safarar Mutane Ga Iyayensu

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
tallafi

Wuraren Bayar Da Tallafi Sun Zama Tarkon Mutuwa

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.