ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ibtila’in Mutuwar Almajirai A Kebbi…

by Umar Faruk
2 years ago
kebbi
  • Sai Da Suka Shafe Minti 30 A Binne Kafin Kawo Musu Dauki
  • Halin Da Muka Tsinci Kanmu A Ciki – Malamin Almajiran
  • Jama’a Na Ci Gaba Da Tururuwar Shaida Lamarin
  • Tambayoyin Da Mutane Ke Yi Ga Gwamnatin Kebbi

Al’ummar Jihar Kebbi har ma da sauran sassan Nijeriya sun shiga alhini bayan rasuwar wasu almajirai takwas sakamakon wani dutse da ya yanke ya fado kan almajiran na Makarantar Allon Malam Dan Umma da ke Unguwar Badariya, cikin Karamar Hukumar Birnin Kebbi.

A safiyar ranar Asabar 20 ga watan Afrilun 2024, da misalin karfe 8 na safe ne iftila’in ya auku. Masana sun bayyana cewa tarihi ya nuna akalla dutsen ya kai kimanin shekaru 80 zuwa 100 da fitowa inda yake ta girma har ya mamaye waje mai yawan gaske.

  • Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Fitar Da Miliyan 309.5 Don Tallafawa Ɗaliban Da Ke Karatu a Ƙasashen waje 
  • Jami’an Tsaro sun Ceto Mata Biyu da aka Yi Garkuwa da Su A Kebbi

Haka kuma sun kara da cewa a lokacin da ba a fara amfani da kasar siminti ba sosai a yankin, jama’a da dama suna amfani da burbushin dutsen ne da kasar da yake cakude da shi wajen gina gidaje. Daga baya kuma dutsen ya koma filayen jama’a har ma da yawa sun gina gidajen kwana ta yadda a halin yanzu gidaje ne a ko ina a yankin da hatsarin ya auku.

ADVERTISEMENT

Saboda wannan al’ada ta amfani da kasar dutsen ne, almajiran da suka je hako kasa bisa umarnin malaminsu domin su gyara wasu ramuka da ke dakunansu, suna kan aiki kwatsam dutsen ya yanke ya taushe akalla su 10, inda nan take takwas suka riga mu gidan gaskiya, biyu suka tsira tare da garzayawa da su asibitin tunawa da Sarki Yahaya. Sai dai daga baya daya shi ma ya rasu, zuwa lokacin hada wannan rahoto almajiri daya ne ke jinya.

Rahotanni sun nunar da cewa wadanda hatsarin ya rutsa da su sun kai kimanin minti 30 a binne kafin a kawo musu agajin gaggawa daga jama’ar da ke unguwar.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

Almajiran da suka rasa rayukansu a nan take da suka hada da Muhammad Bawada, Musa Kambaza, Dan Sayyada Kambaza, Nasiru Cheberu, dukkansu sun fito ne daga Karamar Hukumar Gwandu, sai kuma Yakubu da Aminu da sauransu da suka fito daga wurare daban-daban. Dukkan almajiran da suka rasa rayukansu babu wanda ya kai shekara 20 da haihuwa.

Binciken wakilinmu ya gano cewa wannan shi ne hatsari na farkon a tahirin fitowar dutsen duk da cewa mafi yawan gidajen jama’ar Unguwar Badariya da kewaye duk da kasar dutsen ne aka gina su amma ba a sumu irin wannan ba sai a kan wadannan almajiran.

Da yake tsokaci kan lamarin, malamin almajiran, Malam Dan Umma ya tabbatar da mutuwar almajiran takwas nan take, kana ya kara da cewa, “Yau daya ce daga cikin ranaku mafi bakin ciki a rayuwata. Abin da ya faru shi ne, na ba su umarnin cewa su je su gino kasar don gyara ramukan da ke cikin dakunansu saboda ruwan damina na zuwa. Daga nan sai suka tafi bakin dutsen da ke kusa da makarantar.

“Bayan mintoti kafin dawowarsu, sai wasu daga cikin almajiran suka sheko da gudu suna wayyo, wayyo, dutse ya taushe almajirai da suke ginar kasar a cikin dutsen. A nan take na garzaya wurin da lamarin ya faru, inda na tabbatar da mutuwarsu yayin da biyu da suka tsira kuma aka garzaya da su asibiti don tabbatarwa ko akasin hakan.”

Malam Dan Umma ya ci gaba da cewa, an ajiye gawarwakin almajiran da suka rasu a dakin ajiyar gawa na asibitin tunawa da Sarki Yahaya da ke Birnin Kebbi, kafin a kai su gidajen iyayensu domin yi musu jana’iza.
Bayan faruwar lamarin jama’ar unguwar Badariya da ma na cikin garin Birnin Kebbina ci gaba da tattaki zuwa bakin dutsen don gane wa idanunsu irin yadda lamarin ya faru.

Wasu da suka zanta da wakilinmu, sun bayyana ra’ayin cewa bai kamata a ce malamin almajiran ya ba su umarnin su je su hako kasar gyaran dakunansu ba, saboda kananan yara ne kuma wajen da suke kwana mallakin malamin don haka shi ya kamata ya gyara ba almajiran ba.

Sun kara da fadin cewa idan damina ta kankama, ruwa na gaggarowa daga dutsen zuwa cikin gidajen mutane saboda wasu gidajen a bisa hanyar ruwan daminar aka gina su. Ta hakan ne ake yawan samun matsalolin ambaliya da ke lakume rayukkan jama’a da kuma rasa matsuguni wanda sai sun nemi agajin gaggawa daga gwamnati da kuma wasu hukumomi masu ba da agajin gaggawa idan aka samu ambaliyar ruwan sama.

Wakazalika, abin da mutane ke kara tambaya a kai shi ne, mutanen da ke zama kusa da dutsen sun samu izinin haka kuwa sannan hukumar kula da filaye da ta bunkasa birane sun yi la’akari da irin hadurran da ke tattare da zama a wannan wurin kuwa?

A halin yanzu dai jama’a sun zura ido su ga wane irin mataki ne Gwamnatin Jihar Kebbi za ta dauka domin riga-kafin lamarin a gaba.

kebbi
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Sace ‘Yan Makarantar Mata Ta Kebbi: Abubuwan Da Ba A Fada Ba
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

MASU ALAKA

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi
Manyan Labarai

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

July 7, 2026
Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci
Manyan Labarai

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

July 7, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz
Manyan Labarai

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Next Post
tallafi

Wuraren Bayar Da Tallafi Sun Zama Tarkon Mutuwa

LABARAI MASU NASABA

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

July 7, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

July 7, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

July 7, 2026
Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026
Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

July 7, 2026
'yansanda

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

July 7, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.