ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Arsenal Ta Barar Da Damarta Ta Lashe Firimiya?

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Arsenal

Magoya bayan kungiyar kwallon kafa ta Arsenal dai ba su ji dadin sakamakon wasansu da kungiyar kwallon kafa ta Aston Billa ba sai dai har yanzu magoya bayan suna da yakinin Arsenal din za ta iya lashe gasar har yanzu.

A ranar Lahadi ne dai kungiyar kwallon kafa ta Arsenal ta barar da damar hawa kan teburin Premier League, bayan da ta yi rashin nasara 2-0 a hannun Aston Billa a filin wasa na Emirates. Aston Billa, karkashin tsohon kociyan Arsenal, Unai Emery ta doke

  • Amurka Na Fakewa Da Guzuma Domin Harbin Karsana
  • Sharhi: Kokarin Fahimtar Yanayin Tattalin Arzikin Sin Ta Bangarorin Ayyuka Guda 3

Arsenal gida da waje kenan a bana, bayan cin 1-0 ranar 9 ga  Disambar 2023 a filin wasa na Billa Park.

ADVERTISEMENT

An kuma ci Arsenal kwallayen biyu dab da za a tashi ta hannun Leon Bailey a minti na 84 da Ollie Watkins saura minti uku a busa tashi kuma da wannan sakamakon Arsenal mai maki 71 iri daya da na Liberpool ta ukun teburi, Manchester City tana da maki 73 ta dayan teburi da tazarar maki biyu tsakaninsu.

Sai dai tun a ranar Asabar Manchester City ta dura 5-1 a ragar Luton Town a filin wasa na Etihad a ranar Crystal Palace ta ci Liberpool 1-0 a filin wasa na Anfield a karawar mako na 33. Wannan shi ne karon farko da aka ci kungiyar Arsenal a 2024 cikin wasa

LABARAI MASU NASABA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

11 a Premier League, wadda ta tashi ba ci da Manchester City, sannan ta lashe sauran wasannin gaba daya.

Rabon da Arsenal ta dauki gasar Premier League tun kakar wasa ta 2003 zuwa 2004 mai 13 jimilla, tun daga nan ba ta sake lashe kofin ba hakan ya sa magoya bayan kungiyar suke yunwar lashe gasar.

Kungiyar Arsenal ta kare kakar bara ba tare da daukar kofi ba, bayan da Manchester City ta sha gaban Arsenal a Premier daga karshe-karshen gasar sannan hakan ya bai wa Manchester City damar lashe kofi uku ciki har da na FA Cup da kuma KofinZakarun Turai karon farko a tarihi.

Saura wasanni shida da Arsenal za ta buga nan gaba, ciki har da karawa da Chelsea da Tottenham da kuma Manchester United, inda ake tunanin za ta iya sake barar da maki.

Wasannin da suke gaban Arsenal a Premier League:

20 ga Afirilu – Wolbes ( Molineud) 23 ga Afirilu – Chelsea (Emirates) 28 ga Afirilu – Tottenham (Tottenham Stadium) 4 ga Mayu – Bournemouth (Emirates) 12 ga Mayu- Manchester United (Old Trafford) 19 ga Mayu – Eberton (Emirate) Tasirin Magoya Baya

Bayan da kungiyar kwallon kafa ta Aston Billa ta zura kwallo ta biyu a ragar Arsenal a filin wasa na Fly Emirates, magoya bayan kungiyar Arsenal sun dinga ficewa daga filin tun kafin alkalin wasa ya tashi daga wasan wanda hakan koma baya ne ga kokarin kungiyar na lashe gasar firimiya. Tsohon dan wasan Arsenal, Ian Right, ya soki matakin magoya bayan na ficewa daga filin tun kafin a tashi inda yace kwata-kwata bai kamata ba kuma hakan zai karyarwa da ‘yan wasa gwiwa. Right ya bayar da misali da magoya bayan kungiyar kwallon kafa ta Manchester United da ba sa fita har sai alkalin wasa ya tashi daga wasa saboda suna ganin indai har ba a tashi ba tabbas ‘yan wasan kungiyar za su iya faranta musu rai ta hanyar zura kwallo a raga.

Arsenal
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?
  • Abba Ibrahim Wada
    Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji
  • Abba Ibrahim Wada
    Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City

MASU ALAKA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
Wasanni

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
Wasanni

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Wasanni

Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu

July 11, 2026
Next Post
Sin Ta Nuna Rashin Gamsuwa Da Barazanar Da Amurka Ta Yi Na Kara Haraji Kan Karafa Da Gorar Ruwa Dake Shiga Kasar Daga Kasar Sin

Sin Ta Nuna Rashin Gamsuwa Da Barazanar Da Amurka Ta Yi Na Kara Haraji Kan Karafa Da Gorar Ruwa Dake Shiga Kasar Daga Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.