ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Arsenal Ta Barar Da Damarta Ta Lashe Firimiya?

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Arsenal

Magoya bayan kungiyar kwallon kafa ta Arsenal dai ba su ji dadin sakamakon wasansu da kungiyar kwallon kafa ta Aston Billa ba sai dai har yanzu magoya bayan suna da yakinin Arsenal din za ta iya lashe gasar har yanzu.

A ranar Lahadi ne dai kungiyar kwallon kafa ta Arsenal ta barar da damar hawa kan teburin Premier League, bayan da ta yi rashin nasara 2-0 a hannun Aston Billa a filin wasa na Emirates. Aston Billa, karkashin tsohon kociyan Arsenal, Unai Emery ta doke

  • Amurka Na Fakewa Da Guzuma Domin Harbin Karsana
  • Sharhi: Kokarin Fahimtar Yanayin Tattalin Arzikin Sin Ta Bangarorin Ayyuka Guda 3

Arsenal gida da waje kenan a bana, bayan cin 1-0 ranar 9 ga  Disambar 2023 a filin wasa na Billa Park.

ADVERTISEMENT

An kuma ci Arsenal kwallayen biyu dab da za a tashi ta hannun Leon Bailey a minti na 84 da Ollie Watkins saura minti uku a busa tashi kuma da wannan sakamakon Arsenal mai maki 71 iri daya da na Liberpool ta ukun teburi, Manchester City tana da maki 73 ta dayan teburi da tazarar maki biyu tsakaninsu.

Sai dai tun a ranar Asabar Manchester City ta dura 5-1 a ragar Luton Town a filin wasa na Etihad a ranar Crystal Palace ta ci Liberpool 1-0 a filin wasa na Anfield a karawar mako na 33. Wannan shi ne karon farko da aka ci kungiyar Arsenal a 2024 cikin wasa

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

11 a Premier League, wadda ta tashi ba ci da Manchester City, sannan ta lashe sauran wasannin gaba daya.

Rabon da Arsenal ta dauki gasar Premier League tun kakar wasa ta 2003 zuwa 2004 mai 13 jimilla, tun daga nan ba ta sake lashe kofin ba hakan ya sa magoya bayan kungiyar suke yunwar lashe gasar.

Kungiyar Arsenal ta kare kakar bara ba tare da daukar kofi ba, bayan da Manchester City ta sha gaban Arsenal a Premier daga karshe-karshen gasar sannan hakan ya bai wa Manchester City damar lashe kofi uku ciki har da na FA Cup da kuma KofinZakarun Turai karon farko a tarihi.

Saura wasanni shida da Arsenal za ta buga nan gaba, ciki har da karawa da Chelsea da Tottenham da kuma Manchester United, inda ake tunanin za ta iya sake barar da maki.

Wasannin da suke gaban Arsenal a Premier League:

20 ga Afirilu – Wolbes ( Molineud) 23 ga Afirilu – Chelsea (Emirates) 28 ga Afirilu – Tottenham (Tottenham Stadium) 4 ga Mayu – Bournemouth (Emirates) 12 ga Mayu- Manchester United (Old Trafford) 19 ga Mayu – Eberton (Emirate) Tasirin Magoya Baya

Bayan da kungiyar kwallon kafa ta Aston Billa ta zura kwallo ta biyu a ragar Arsenal a filin wasa na Fly Emirates, magoya bayan kungiyar Arsenal sun dinga ficewa daga filin tun kafin alkalin wasa ya tashi daga wasan wanda hakan koma baya ne ga kokarin kungiyar na lashe gasar firimiya. Tsohon dan wasan Arsenal, Ian Right, ya soki matakin magoya bayan na ficewa daga filin tun kafin a tashi inda yace kwata-kwata bai kamata ba kuma hakan zai karyarwa da ‘yan wasa gwiwa. Right ya bayar da misali da magoya bayan kungiyar kwallon kafa ta Manchester United da ba sa fita har sai alkalin wasa ya tashi daga wasa saboda suna ganin indai har ba a tashi ba tabbas ‘yan wasan kungiyar za su iya faranta musu rai ta hanyar zura kwallo a raga.

Arsenal
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Yaushe Za A Fara Kofin Zakarun Turai
  • Abba Ibrahim Wada
    Messi Ya Yi Ritaya A Argentina: Da Me Za Mu Iya Tuna Gwarzon Duniyar?
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye ‘Yan wasan Nijeriya Da Za Su Buga Gasar Firimiyar Ingila Ta Bana?
  • Abba Ibrahim Wada
    Chelsea A Ƙarƙashin Xavi Alonso

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
Wasanni

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

September 8, 2026
Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
Wasanni

Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain

September 7, 2026
Next Post
Sin Ta Nuna Rashin Gamsuwa Da Barazanar Da Amurka Ta Yi Na Kara Haraji Kan Karafa Da Gorar Ruwa Dake Shiga Kasar Daga Kasar Sin

Sin Ta Nuna Rashin Gamsuwa Da Barazanar Da Amurka Ta Yi Na Kara Haraji Kan Karafa Da Gorar Ruwa Dake Shiga Kasar Daga Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.