• English
  • Business News
Thursday, June 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Suka Gudana A Zanga-zangar Cire Tallafin Mai

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
Abubuwan Da Suka Gudana A Zanga-zangar Cire Tallafin Mai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan an kasa cimma matsaya a tsakanin gwamnatin tarayya da kuma kungiyar kwadugo (NLC) na tsawan kwanaki biyu, kungiyar kwadugo tare da hadin gwiwar shugabannin kungiyar ‘yan kasuwa (TUC) sun gudanar da zanga-zangar adawa da cire tallafin mai a dukkan fadin kasar nan.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da sabuwar gwamnatin tarayya karkashin jagorancin Bola Ahmed Tinubu ta fara dandana zafin yajin aiki, domin a makon da ya gabata kungiyar likitoci ta tsunduma cikin yajin aikin sai baba ta gani sakamakon kin biya musu bukatocinsu, inda a yanzu kuma kungiyar NLC na gudanar da yajin aiki tare da zanga-zangar adawa da cire tallafin mai.

  • Gwarzo, Bagudu Da Matawalle Na Cikin Jerin Ministocin Tinubu, Kashi Na Biyu
  • An Fara Taron Harkokin Sufurin Jiragen Sama Ta 2023 A HK

Yajin aiki tare da zanga-zangar da kungiyar kwadugo ta shirya ya fara aiki ne tun a ranar Laraba domin nuna wa gwamnatin tarayya adawa da cire tallafin mai da ya haifar da tsadar rayuwa a fadin kasar nan.

Ko a ranar Talata, ma’aikatan mai sun gudanar da zanga-zanga tare da rufe ofishin hukumar kula da harkokin mai na kasa da ke Legas, yayin da kuma suka sha alwashin rufe ofisoshin hukumar a fadin kasar.

Da yake magana kan yajin aikin, Shugaban NLC, Joe Ajaero, ya ce kungiyoyin kwadugon ba za su dakatar da zanga-zangar da yajin aikin da suka shirya yi na kasar nan ba har sai gwamnati ta biya musu bukato-cinsu.

Labarai Masu Nasaba

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

Ajaero ya bayyana haka ne sa’o’i kadan bayan wani taron tattaunawa da kwamitin da shugaban kasa ya kafa a fadarsa da ke Abuja, ya gagara yin sulhu.

Gwamnatin tarayya dai ta yi wani yunkuri na dakile yajin aikin da zanga-zanga wanda ta gana da shugabannin kungiyoyin NLC da TUC a ranar Litinin da ta gabata, amma kuma lamarin ya ci tura.

Idan ba a manta ba dai an samu sabani tsakanin gwamnatin tarayya da kungiyoyin kwadago biyo bayan cire tallafin man fetur da Shugaba Tinubu yayi a ranar 29 ga watan Mayu 2023.

A kokarin da gwamnatin ke yi na samar da sahalaha, gwamnati ta kafa wani kwamiti da zai duba bukatun kungiyoyin kwadugo na neman karin albashin kashi 300 domin bai wa ma’aikata damar tun-karar kalubalen tabarbarewar tattalin arzikin da ya biyo bayan cire tallafin mai.

Duk da cewa an bai wa kwamatin tsawon makonni takwas domin ya fito da tsarin da ya dace ga ma’aikata da ‘yan Nijeriya baki daya, shugabannin kungiyar kwadugon sun dage cewa kwamitin ya ci gaba da nuna rashin jajircewa wajen cimma burinsu.

Matakin farko da shugabannin kwadugo suka yi na shiga yajin aikin ya hadu da fushin kotu wanda ta hana kungiyar.

Da yake jawabi tun da farko bayan ganawar da jami’an gwamnatin tarayya, babban sakataren kungiyar ta NLC, Emmanuel Ugboaja, ya yi nuni da cewa tattaunawar bai samu cimma matsaya ba.

Sai dai mataimakin shugaban kungiyar ta NLC, Titus Amba ya bayyana cewa babu wani sabon abu da aka samu biyo bayan jawabin Shugaban Tinubu da ya yi a yammacin ranar Litinin.

Ya ce Tinubu ya kaddamar da tallafi na naira biliyan 500 wanda za a raba wa masana’antun da kananan ‘yan kasuwa da manoma.

A yayin gudanar da wannan zanga-zangar, mambobin kungiyoyin NLC da na TUC da kungiyoyin farar hula, sun bijire wa shingen tsaro tare da karya kofar shiga majalisar wakilai domin shiga harabar majalisar, don nuna adawa da cire tallafin man fetur da gwamnatin tarayya ta yi.

Majalisar dattawa ta kafa wani kwamiti da zai tattauna da kungiyoyin ma’aikata da suka yi zanga-zanga bayan sun tilastawa ciki harabar majalisar dokokin kasar don nuna rashin amincewarsu da cire tallafin man fetur da gwamnatin tarayya ta yi.

Masu zanga-zangar sun yi tattaki ne tun daga ‘Unity Fountain’ da ke Abuja har zuwa harabar majalisar dokokin kasar domin nuna adawa da manufofin gwamnatin Shugaba Tinubu na cire tallafin mai.

Nan take Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya shiga wata ganawar sirri da ‘yan majalisar, kuma da fitowar sa daga ganawar, ya ce majalisar dattawa ta kafa wani kwamiti mai mutane uku da zai gana da masu zanga-zangar a harabar zauren majalisar.

Kwamitin ya samu jagorancin shugaban masu rinjaye na majalisar dattawa, Sanata Ali Ndume, mai wakiltar mazabar Borno ta Kudu da Sanata mai wakiltar Abuja, Heebah Ireti Kingibe da Sanatan Anam-bra ta Kudu, Tony Nwoye da dai sauransu.

Majalisar dattawan ta kuma kuduri aniyar cewa nan da dan kankanin lokaci za ta gana da shugabannin NLC da TUC domin ganin an shawo kan matsalar da ake fama da ita a halin yanzu.

An ga sanatocin suna tattaunawa da Shugaban kungiyar NLC, Joe Ajaero da takwaransa na kungiyar TUC, Festus Osifo.

Kungiyoyin kwadugon da suka hada da TUC da sauran kungiyoyin sun fara gudanar da zanga-zanga a Babban Birnin Tarayya Abuja, da sauran jihohin tarayyar kasar da suka hada da Legas, Abiya, Filato, Ka-duna, Kano, Ribas, Zamfara, Katsina, Kuros Ribas, Ebonyi, Inugu, Kwara, Ogun, Imo, Ondo, da Edo, da dai sauransu.

Wakilinmu Jihar Kano Abdullahi Sheka ya ruwaito mana cewa, kamar sauran takororinta na fadin kasa baki daya, an gudanar da zanga-zangar lumana wanda shugaban kungiyar NLC reshen Jihar Kano, Kwamared Kabiru Munjibir ya jagoranta, a lokacin da yake gabatar sakon kungiyar ga gwamna zuwa ga Shugaban Tinubu, na nuna adawa da cire tallafin mai.

Shi ma wakilinmu na Jihar Nasarawa, Zubairu M Lawal ya labarta mana cewa, kungiyar kwadugo ta kasa reshen Jihar Nasarawa tabi sahun takwarorinta na jihohi 36 da ke fadin tarayyar Nijariya wajen gudanar da zanga-zangar rashin amincewa da cire tallafin man fetur.

Zanga-zangar da ya gudana a Lafiya fadar Gwamnatin Jihar Nasarawa ya taso ne daga Mahadar Total zuwa harabar ofishin mataimakin gwamnan Jihar Nasarawa.

Da yake jawabi Shugaban kungiyar kwadago reshen Jihar Nasarawa, Kwamared Isma’ila Ayuba Oko, ya ce kuddurin gwamnatin Tinubu ta zoma ‘yan Nijariya da cutarwa.

Zangar-zangar kungiyar kwadago a Jihar Nasarawa


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Rufe Iyakokin Nijeriya Da Nijar

Next Post

Nijar Ta Yanke Hulda Tsakaninta Da Nijeriya

Related

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji
Manyan Labarai

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

2 hours ago
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…
Ra'ayi Riga

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

2 hours ago
Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

4 hours ago
Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga
Labarai

Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

5 hours ago
Kawayen amarya
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina

8 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Labarai

Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja

10 hours ago
Next Post
Nijar Ta Yanke Hulda Tsakaninta Da Nijeriya

Nijar Ta Yanke Hulda Tsakaninta Da Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

June 26, 2025
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

June 26, 2025
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

June 26, 2025
Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

June 26, 2025
Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

June 26, 2025
Kawayen amarya

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina

June 26, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja

June 26, 2025
Tinubu

Tinubu Zai Rattaba Hannu Kan Kudirorin Sauya Fasalin Haraji 4 A Yau Alhamis 

June 26, 2025
Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

June 25, 2025
Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

June 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.