• English
  • Business News
Monday, June 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Suka Kamata A Sani Kan Noman Gyada

by Abubakar Abba
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
Abubuwan Da Suka Kamata A Sani Kan Noman Gyada
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Manoman gyada za su iya sa wa a tatse musu man jikinta tas, su sayar tare da samun gwaggwabar riba, duk da dai ya danganta da yawan gyadar da aka tatse man nata.

Ko shakka babu, ana matukar samun riba a noman gyada, dalili kuwa duk manomin da zai iya noma kadada daya, to kuwa zai iya samun akalla tan biyar.

Kalubalen Da Manoman Gyada Ke Fuskanta:

Akwai rashin kayan noman gyada na zamani da kuma rashin sanin kasuwar da ta dace manoma su kai domin sayarwa tare da rashin samar da hukumar da take tantance farashin amfanin gonar.

Har ila yau, akwai kuma kalubalen samun kyakkyawan yanayi maras dadi, wanda hakan ke shafar noman nata tare da rashin wadatattun kudade a hannun manoman, kana kuma da rashin kayan noma na zamani, musamman ganin cewa; akasarin manoman gyadar masu karamin karfi ne.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

Wadannan kalubale da sauransu, ya sa suke ci gaba da yin noman gyadar ta hanyar yin amfani da kayan noma na gargajiya.

Wace Jiha Ce A Nijeriya Ke Kan Gaba Wajen Noman Gyada?

Bincike ya tabbatar da cewa, Jihar Biniwe ce a fadin wannan kasa ke kan gaba wajen noman gyada, domin kuwa a shekarar 2005, manoma a jihar sun noma kimanin tan dubu 358,6 1000.

Har ila yau, wannan adadi ya bayyana jihar a matsayin wadda ta noma kimanin kashi 13.68 a cikin 100 a duk fadin Nijeriya.

Matakan Da Manoman Gyada Za Su Dauka Yayin Noma Ta:

Zabar Gonar Da Za Su Shuka Ta:

Wannnan shi ne mataki na farko da ake bukatar manomi ya fara da shi kafin fara yin noman gadan-gadan, musamman domin tabbatar da kasar noman ita ce wacce ta fi dacewa ya yi noman gyadar da ita.

Lokacin Shukata:

A nan manomi zai fara yin shuka ne, a lokacin da kasar noman ke da danshi, musamman a kakar noman damina, inda a lokacin yin shukar ake bukatar ya zuba mata takin gargajiya, don amfanin ya kara habaka.

Lokacin Yi Mata Girbi:

Yi wa gyada girbi na da matukar wahala, sannan ana kashe kudade da dama, haka kazalika ta na kai wa daga wata hudu zuwa Biyar kafin ta nuna baki-daya, inda kuma ake girbin ta yayin da ganyenta ya fara sauyawa zuwa kalar ruwan kasa.

Har ila yau, bayan an girbe ta, ana bayar da shawarar adana ta a inda ba za ta lalace ba, sannan kuma bayan yin girbin za a iya sake yin wata sabuwar shukar; duk a cikin kakar wannan shekarar da aka yi noman gyadar aka yi girbi.

Ban Ruwa:

Ana iya amfani da fanfon ban ruwa wajen yi wa gyada ban ruwa, inda wannan hanya ce tafi saukin yin ban ruwan ga manoman gyadar.

Buhun Gyada Nawa Ake Samu A Duk Kadada Guda?

A duk kadadar noma daya, ana samun buhun gyada daga uku zuwa takwas, inda kuma take kai wa watanni uku kafin a girbe ta, haka nan an fi son a shuka gyadar da ake kira a turance ‘Manipinta’, musamman ganin cewa, ita ce nau’in babba; sakamakon yawan amfanin da ake samu daga gare ta, sannan a duk kadada daya ana samun buhu goma sha biyu.

Mafi yawan lokuta, idan aka yi girbin gyada lokacin rani, sakamakon gwajin da aka samu ya tabbatar da cewa, ana iya samun daga tan .8 zuwa tan 1.8 a duk kadada guda.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Noman alkamaNoman gurjiyaShukar Masara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Kafa Majalisar Dattawan Kano

Next Post

AFCON 2023: ‘Yan Wasan Da Za Su Haskaka A Gasar Kofin Afirka

Related

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

2 days ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

2 days ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

2 days ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

1 week ago
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi

1 week ago
Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

2 weeks ago
Next Post
AFCON

AFCON 2023: ‘Yan Wasan Da Za Su Haskaka A Gasar Kofin Afirka

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

June 1, 2025
Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

June 1, 2025
Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara

Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara

June 1, 2025
Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka

Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka

June 1, 2025
Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

June 1, 2025
Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

June 1, 2025
Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

June 1, 2025
bakin wake

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

June 1, 2025
‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

June 1, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

June 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.