• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Suka Kamata A Sani Kan Noman Gyada

by Abubakar Abba
2 years ago
Noman Gyada

Manoman gyada za su iya sa wa a tatse musu man jikinta tas, su sayar tare da samun gwaggwabar riba, duk da dai ya danganta da yawan gyadar da aka tatse man nata.

Ko shakka babu, ana matukar samun riba a noman gyada, dalili kuwa duk manomin da zai iya noma kadada daya, to kuwa zai iya samun akalla tan biyar.

Kalubalen Da Manoman Gyada Ke Fuskanta:

Akwai rashin kayan noman gyada na zamani da kuma rashin sanin kasuwar da ta dace manoma su kai domin sayarwa tare da rashin samar da hukumar da take tantance farashin amfanin gonar.

Har ila yau, akwai kuma kalubalen samun kyakkyawan yanayi maras dadi, wanda hakan ke shafar noman nata tare da rashin wadatattun kudade a hannun manoman, kana kuma da rashin kayan noma na zamani, musamman ganin cewa; akasarin manoman gyadar masu karamin karfi ne.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

Wadannan kalubale da sauransu, ya sa suke ci gaba da yin noman gyadar ta hanyar yin amfani da kayan noma na gargajiya.

Wace Jiha Ce A Nijeriya Ke Kan Gaba Wajen Noman Gyada?

Bincike ya tabbatar da cewa, Jihar Biniwe ce a fadin wannan kasa ke kan gaba wajen noman gyada, domin kuwa a shekarar 2005, manoma a jihar sun noma kimanin tan dubu 358,6 1000.

Har ila yau, wannan adadi ya bayyana jihar a matsayin wadda ta noma kimanin kashi 13.68 a cikin 100 a duk fadin Nijeriya.

Matakan Da Manoman Gyada Za Su Dauka Yayin Noma Ta:

Zabar Gonar Da Za Su Shuka Ta:

Wannnan shi ne mataki na farko da ake bukatar manomi ya fara da shi kafin fara yin noman gadan-gadan, musamman domin tabbatar da kasar noman ita ce wacce ta fi dacewa ya yi noman gyadar da ita.

Lokacin Shukata:

A nan manomi zai fara yin shuka ne, a lokacin da kasar noman ke da danshi, musamman a kakar noman damina, inda a lokacin yin shukar ake bukatar ya zuba mata takin gargajiya, don amfanin ya kara habaka.

Lokacin Yi Mata Girbi:

Yi wa gyada girbi na da matukar wahala, sannan ana kashe kudade da dama, haka kazalika ta na kai wa daga wata hudu zuwa Biyar kafin ta nuna baki-daya, inda kuma ake girbin ta yayin da ganyenta ya fara sauyawa zuwa kalar ruwan kasa.

Har ila yau, bayan an girbe ta, ana bayar da shawarar adana ta a inda ba za ta lalace ba, sannan kuma bayan yin girbin za a iya sake yin wata sabuwar shukar; duk a cikin kakar wannan shekarar da aka yi noman gyadar aka yi girbi.

Ban Ruwa:

Ana iya amfani da fanfon ban ruwa wajen yi wa gyada ban ruwa, inda wannan hanya ce tafi saukin yin ban ruwan ga manoman gyadar.

Buhun Gyada Nawa Ake Samu A Duk Kadada Guda?

A duk kadadar noma daya, ana samun buhun gyada daga uku zuwa takwas, inda kuma take kai wa watanni uku kafin a girbe ta, haka nan an fi son a shuka gyadar da ake kira a turance ‘Manipinta’, musamman ganin cewa, ita ce nau’in babba; sakamakon yawan amfanin da ake samu daga gare ta, sannan a duk kadada daya ana samun buhu goma sha biyu.

Mafi yawan lokuta, idan aka yi girbin gyada lokacin rani, sakamakon gwajin da aka samu ya tabbatar da cewa, ana iya samun daga tan .8 zuwa tan 1.8 a duk kadada guda.

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Ɓarayi 13 Tare Da Ƙwato Shanu 27 A Kaduna
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

October 18, 2025
Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI
Noma Da Kiwo

Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

October 18, 2025
Next Post
AFCON

AFCON 2023: ‘Yan Wasan Da Za Su Haskaka A Gasar Kofin Afirka

LABARAI MASU NASABA

Asuu

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025
Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

October 29, 2025
Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

October 29, 2025
An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

October 29, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

October 29, 2025
An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

October 29, 2025
Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

October 29, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

October 29, 2025
COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

October 29, 2025
Binciken ‘Yan Sanda Kan Wanda Ake Zargi Da Tawayen “‘Yancin Kan Taiwan” Mataki Ne Na Adalci Don Kare Hadin Kan Kasa

Binciken ‘Yan Sanda Kan Wanda Ake Zargi Da Tawayen “‘Yancin Kan Taiwan” Mataki Ne Na Adalci Don Kare Hadin Kan Kasa

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.