• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Suka Kamata A Sani Kan Noman Gyada

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Abubuwan Da Suka Kamata A Sani Kan Noman Gyada
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Manoman gyada za su iya sa wa a tatse musu man jikinta tas, su sayar tare da samun gwaggwabar riba, duk da dai ya danganta da yawan gyadar da aka tatse man nata.

Ko shakka babu, ana matukar samun riba a noman gyada, dalili kuwa duk manomin da zai iya noma kadada daya, to kuwa zai iya samun akalla tan biyar.

Kalubalen Da Manoman Gyada Ke Fuskanta:

Akwai rashin kayan noman gyada na zamani da kuma rashin sanin kasuwar da ta dace manoma su kai domin sayarwa tare da rashin samar da hukumar da take tantance farashin amfanin gonar.

Har ila yau, akwai kuma kalubalen samun kyakkyawan yanayi maras dadi, wanda hakan ke shafar noman nata tare da rashin wadatattun kudade a hannun manoman, kana kuma da rashin kayan noma na zamani, musamman ganin cewa; akasarin manoman gyadar masu karamin karfi ne.

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Wadannan kalubale da sauransu, ya sa suke ci gaba da yin noman gyadar ta hanyar yin amfani da kayan noma na gargajiya.

Wace Jiha Ce A Nijeriya Ke Kan Gaba Wajen Noman Gyada?

Bincike ya tabbatar da cewa, Jihar Biniwe ce a fadin wannan kasa ke kan gaba wajen noman gyada, domin kuwa a shekarar 2005, manoma a jihar sun noma kimanin tan dubu 358,6 1000.

Har ila yau, wannan adadi ya bayyana jihar a matsayin wadda ta noma kimanin kashi 13.68 a cikin 100 a duk fadin Nijeriya.

Matakan Da Manoman Gyada Za Su Dauka Yayin Noma Ta:

Zabar Gonar Da Za Su Shuka Ta:

Wannnan shi ne mataki na farko da ake bukatar manomi ya fara da shi kafin fara yin noman gadan-gadan, musamman domin tabbatar da kasar noman ita ce wacce ta fi dacewa ya yi noman gyadar da ita.

Lokacin Shukata:

A nan manomi zai fara yin shuka ne, a lokacin da kasar noman ke da danshi, musamman a kakar noman damina, inda a lokacin yin shukar ake bukatar ya zuba mata takin gargajiya, don amfanin ya kara habaka.

Lokacin Yi Mata Girbi:

Yi wa gyada girbi na da matukar wahala, sannan ana kashe kudade da dama, haka kazalika ta na kai wa daga wata hudu zuwa Biyar kafin ta nuna baki-daya, inda kuma ake girbin ta yayin da ganyenta ya fara sauyawa zuwa kalar ruwan kasa.

Har ila yau, bayan an girbe ta, ana bayar da shawarar adana ta a inda ba za ta lalace ba, sannan kuma bayan yin girbin za a iya sake yin wata sabuwar shukar; duk a cikin kakar wannan shekarar da aka yi noman gyadar aka yi girbi.

Ban Ruwa:

Ana iya amfani da fanfon ban ruwa wajen yi wa gyada ban ruwa, inda wannan hanya ce tafi saukin yin ban ruwan ga manoman gyadar.

Buhun Gyada Nawa Ake Samu A Duk Kadada Guda?

A duk kadadar noma daya, ana samun buhun gyada daga uku zuwa takwas, inda kuma take kai wa watanni uku kafin a girbe ta, haka nan an fi son a shuka gyadar da ake kira a turance ‘Manipinta’, musamman ganin cewa, ita ce nau’in babba; sakamakon yawan amfanin da ake samu daga gare ta, sannan a duk kadada daya ana samun buhu goma sha biyu.

Mafi yawan lokuta, idan aka yi girbin gyada lokacin rani, sakamakon gwajin da aka samu ya tabbatar da cewa, ana iya samun daga tan .8 zuwa tan 1.8 a duk kadada guda.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Noman alkamaNoman gurjiyaShukar Masara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Kafa Majalisar Dattawan Kano

Next Post

AFCON 2023: ‘Yan Wasan Da Za Su Haskaka A Gasar Kofin Afirka

Related

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

7 days ago
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON
Noma Da Kiwo

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

7 days ago
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

3 weeks ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

3 weeks ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

4 weeks ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

4 weeks ago
Next Post
AFCON

AFCON 2023: ‘Yan Wasan Da Za Su Haskaka A Gasar Kofin Afirka

LABARAI MASU NASABA

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.