ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Suka Kamata A Sani Kan Noman Gyada

by Abubakar Abba
2 years ago
Noman Gyada

Manoman gyada za su iya sa wa a tatse musu man jikinta tas, su sayar tare da samun gwaggwabar riba, duk da dai ya danganta da yawan gyadar da aka tatse man nata.

Ko shakka babu, ana matukar samun riba a noman gyada, dalili kuwa duk manomin da zai iya noma kadada daya, to kuwa zai iya samun akalla tan biyar.

Kalubalen Da Manoman Gyada Ke Fuskanta:

ADVERTISEMENT

Akwai rashin kayan noman gyada na zamani da kuma rashin sanin kasuwar da ta dace manoma su kai domin sayarwa tare da rashin samar da hukumar da take tantance farashin amfanin gonar.

Har ila yau, akwai kuma kalubalen samun kyakkyawan yanayi maras dadi, wanda hakan ke shafar noman nata tare da rashin wadatattun kudade a hannun manoman, kana kuma da rashin kayan noma na zamani, musamman ganin cewa; akasarin manoman gyadar masu karamin karfi ne.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Wadannan kalubale da sauransu, ya sa suke ci gaba da yin noman gyadar ta hanyar yin amfani da kayan noma na gargajiya.

Wace Jiha Ce A Nijeriya Ke Kan Gaba Wajen Noman Gyada?

Bincike ya tabbatar da cewa, Jihar Biniwe ce a fadin wannan kasa ke kan gaba wajen noman gyada, domin kuwa a shekarar 2005, manoma a jihar sun noma kimanin tan dubu 358,6 1000.

Har ila yau, wannan adadi ya bayyana jihar a matsayin wadda ta noma kimanin kashi 13.68 a cikin 100 a duk fadin Nijeriya.

Matakan Da Manoman Gyada Za Su Dauka Yayin Noma Ta:

Zabar Gonar Da Za Su Shuka Ta:

Wannnan shi ne mataki na farko da ake bukatar manomi ya fara da shi kafin fara yin noman gadan-gadan, musamman domin tabbatar da kasar noman ita ce wacce ta fi dacewa ya yi noman gyadar da ita.

Lokacin Shukata:

A nan manomi zai fara yin shuka ne, a lokacin da kasar noman ke da danshi, musamman a kakar noman damina, inda a lokacin yin shukar ake bukatar ya zuba mata takin gargajiya, don amfanin ya kara habaka.

Lokacin Yi Mata Girbi:

Yi wa gyada girbi na da matukar wahala, sannan ana kashe kudade da dama, haka kazalika ta na kai wa daga wata hudu zuwa Biyar kafin ta nuna baki-daya, inda kuma ake girbin ta yayin da ganyenta ya fara sauyawa zuwa kalar ruwan kasa.

Har ila yau, bayan an girbe ta, ana bayar da shawarar adana ta a inda ba za ta lalace ba, sannan kuma bayan yin girbin za a iya sake yin wata sabuwar shukar; duk a cikin kakar wannan shekarar da aka yi noman gyadar aka yi girbi.

Ban Ruwa:

Ana iya amfani da fanfon ban ruwa wajen yi wa gyada ban ruwa, inda wannan hanya ce tafi saukin yin ban ruwan ga manoman gyadar.

Buhun Gyada Nawa Ake Samu A Duk Kadada Guda?

A duk kadadar noma daya, ana samun buhun gyada daga uku zuwa takwas, inda kuma take kai wa watanni uku kafin a girbe ta, haka nan an fi son a shuka gyadar da ake kira a turance ‘Manipinta’, musamman ganin cewa, ita ce nau’in babba; sakamakon yawan amfanin da ake samu daga gare ta, sannan a duk kadada daya ana samun buhu goma sha biyu.

Mafi yawan lokuta, idan aka yi girbin gyada lokacin rani, sakamakon gwajin da aka samu ya tabbatar da cewa, ana iya samun daga tan .8 zuwa tan 1.8 a duk kadada guda.

 

Noman Gyada
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
AFCON

AFCON 2023: ‘Yan Wasan Da Za Su Haskaka A Gasar Kofin Afirka

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.