• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Za A Rika Tuna Saratu Gidado Da Su A Fagen Fim

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Saratu

Labarin rasuwar marigayiya Saratu Gidado da ta yi suna a fagen fina-finan Hausa (Kannywood) har ma da wasu na turanci da take yi jefi-jefi, ya yi matukar girgiza ba kawai fage.

Fim ba har da sauran al’umma bisa yadda jarumar ta shahara da kuma irin jin kan da ta fara yi ga al’umma ta gidauniyarta.

  • An Bude Baje Kolin Kayayyakin Masarufi Na Kasa Da Kasa Na Sin Karo Na 4
  • ‘Yan Ta’adda Sun Yi Yunƙurin Ƙwace Iko Da Sakatariyar Jihar Oyo

Ita dai Saratu Gidado wacce ta rasu ranar Talata 9 ga Afrilun 2024, an haife ta ce a Jihar Gombe, a ranar 17-01-1968. Sannan ta yi karatu tun daga matakin firamare a jihar Kano. Daso, wadda tayi suna wajen fitowa a matsayin “Ba Sani Ba Sabo” a shirye shiryenta, ta kasance abar so a wajen masu kallo saboda yadda take yin abu da gaske kuma babu tsoro a cikin Shirin Fim.

Daso ta yi suna ne musamman wajen fitowa a matsayin mara tsoro, masifaffiya, da kuma ba sani ba sabo. Wannan shi ne ya sa ta fita daban a cikin ragowar jarumai mata a masana’antar saboda tana iya fitowa a duk yanayin da ake bukata ta fito musamman a matsayin uwa mai tsoratarwa.

Marigayiyar dai ta kasance sananniya a idon duk wani wanda yake Kallon fina-finan Hausa da ma wanda ba ya kallo saboda irin rawar da take takawa sannan kuma ta kasance mace tilo a masana’antar da idan ana bukatar salo na fitowa a uwa ko mace mara kirki ko mara tsoro ko mara tausayi ita ce kadai za ta iya fitowa ta bayar da abinda ake bukata.

LABARAI MASU NASABA

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

Gwarzon Mawaƙin Shekarar 2025, Skales

Har ila yau, ta kasance abar soyuwa a zukatan masu kallo saboda duk da irin ba sani ba sabo da take nunawa amma tana da faran-faran da mutane domin an yi mata shaidar cewa mutuniyar kirki ce.

A shekara ta 2000 ta tsunduma harkokin fina finan hausa, inda ta fara fitowa a cikin Shirin “Linzami Da Wuta” wanda kamfanin Sarauniya ya shirya. Wasu daga cikin fina-finan da ta fito sun hada da ‘Yar Mai Ganye da Nagari da Sansani da Mashi da Fil’azal da Jakar Magori da Gidan Iko da Gidauniya da Uwar Kudi da Gani Ga Ka da kuma Shirin turanci na “There is Way” da kamfanin Jammaje ya shirya.

Shiri na kwana kwanan nan da ya sake fitowa da ita shi ne Shirin LABARINA na kamfanin Saira Mobies, domin an yaba irin rawar da ta taka kuma. A shekara ta 2016 ne Sarkin Kano na 14 Muhammad Sanusi II ya nada ta a matsayin Jakadiya.

Ta kasance mai son taimakawa marayu wajen samar musu abinci da kayan sakawa sannan tana yawan bayyana a shafukan sada zumunta inda take bayyana ra’ayinta a kan abubuwan da ake tattaunawa sannan kuma tana da wata gidauniya ta tallafawa marasa galihu inda ko a cikin watan Ramadana da ya wuce ta rarraba kayan abinci ga marayu da mabukata.

Masu sharhi a kan harkokin fina-finan Hausa dai sun bayyana irin rawar da Daso take takawa a matsayin ta musamman saboda har kawo yanzu babu wata mace da ta taso wadda ake ganin za ta iya maye gurbinta kuma hakan ne ya sa dole idan ana bukatar salo irin nata ita kadai ake iya nema.

Kamar yadda iyalai da ‘yan uwanta suka bayyana, ta rasu da safiyar Talata 9-04-2024  bayan ta dauki azumi na 30, kuma tuni aka yi mata sallah kamar yadda addinin musulunci ya tanada.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
Nishadi

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Mawaƙin Shekarar 2025, Skales

October 25, 2025
Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 
Nishadi

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

October 11, 2025
Next Post
Ko Hana Fina-finan Daba Zai Rage Aikata Laifukan Daba A Kano?

Ko Hana Fina-finan Daba Zai Rage Aikata Laifukan Daba A Kano?

LABARAI MASU NASABA

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025
CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

November 5, 2025
Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.