• English
  • Business News
Monday, June 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Za A Rika Tuna Saratu Gidado Da Su A Fagen Fim

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
in Nishadi
0
Abubuwan Da Za A Rika Tuna Saratu Gidado Da Su A Fagen Fim
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarin rasuwar marigayiya Saratu Gidado da ta yi suna a fagen fina-finan Hausa (Kannywood) har ma da wasu na turanci da take yi jefi-jefi, ya yi matukar girgiza ba kawai fage.

Fim ba har da sauran al’umma bisa yadda jarumar ta shahara da kuma irin jin kan da ta fara yi ga al’umma ta gidauniyarta.

  • An Bude Baje Kolin Kayayyakin Masarufi Na Kasa Da Kasa Na Sin Karo Na 4
  • ‘Yan Ta’adda Sun Yi Yunƙurin Ƙwace Iko Da Sakatariyar Jihar Oyo

Ita dai Saratu Gidado wacce ta rasu ranar Talata 9 ga Afrilun 2024, an haife ta ce a Jihar Gombe, a ranar 17-01-1968. Sannan ta yi karatu tun daga matakin firamare a jihar Kano. Daso, wadda tayi suna wajen fitowa a matsayin “Ba Sani Ba Sabo” a shirye shiryenta, ta kasance abar so a wajen masu kallo saboda yadda take yin abu da gaske kuma babu tsoro a cikin Shirin Fim.

Daso ta yi suna ne musamman wajen fitowa a matsayin mara tsoro, masifaffiya, da kuma ba sani ba sabo. Wannan shi ne ya sa ta fita daban a cikin ragowar jarumai mata a masana’antar saboda tana iya fitowa a duk yanayin da ake bukata ta fito musamman a matsayin uwa mai tsoratarwa.

Marigayiyar dai ta kasance sananniya a idon duk wani wanda yake Kallon fina-finan Hausa da ma wanda ba ya kallo saboda irin rawar da take takawa sannan kuma ta kasance mace tilo a masana’antar da idan ana bukatar salo na fitowa a uwa ko mace mara kirki ko mara tsoro ko mara tausayi ita ce kadai za ta iya fitowa ta bayar da abinda ake bukata.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

Har ila yau, ta kasance abar soyuwa a zukatan masu kallo saboda duk da irin ba sani ba sabo da take nunawa amma tana da faran-faran da mutane domin an yi mata shaidar cewa mutuniyar kirki ce.

A shekara ta 2000 ta tsunduma harkokin fina finan hausa, inda ta fara fitowa a cikin Shirin “Linzami Da Wuta” wanda kamfanin Sarauniya ya shirya. Wasu daga cikin fina-finan da ta fito sun hada da ‘Yar Mai Ganye da Nagari da Sansani da Mashi da Fil’azal da Jakar Magori da Gidan Iko da Gidauniya da Uwar Kudi da Gani Ga Ka da kuma Shirin turanci na “There is Way” da kamfanin Jammaje ya shirya.

Shiri na kwana kwanan nan da ya sake fitowa da ita shi ne Shirin LABARINA na kamfanin Saira Mobies, domin an yaba irin rawar da ta taka kuma. A shekara ta 2016 ne Sarkin Kano na 14 Muhammad Sanusi II ya nada ta a matsayin Jakadiya.

Ta kasance mai son taimakawa marayu wajen samar musu abinci da kayan sakawa sannan tana yawan bayyana a shafukan sada zumunta inda take bayyana ra’ayinta a kan abubuwan da ake tattaunawa sannan kuma tana da wata gidauniya ta tallafawa marasa galihu inda ko a cikin watan Ramadana da ya wuce ta rarraba kayan abinci ga marayu da mabukata.

Masu sharhi a kan harkokin fina-finan Hausa dai sun bayyana irin rawar da Daso take takawa a matsayin ta musamman saboda har kawo yanzu babu wata mace da ta taso wadda ake ganin za ta iya maye gurbinta kuma hakan ne ya sa dole idan ana bukatar salo irin nata ita kadai ake iya nema.

Kamar yadda iyalai da ‘yan uwanta suka bayyana, ta rasu da safiyar Talata 9-04-2024  bayan ta dauki azumi na 30, kuma tuni aka yi mata sallah kamar yadda addinin musulunci ya tanada.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shagulgulan Sallar Bana Da Abin Da Ya Sa Ake Cewa “Ba A Yin Budurwa Da Sallah”

Next Post

Ko Hana Fina-finan Daba Zai Rage Aikata Laifukan Daba A Kano?

Related

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu
Nishadi

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

1 day ago
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 
Nishadi

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

1 week ago
Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani
Nishadi

Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani

2 weeks ago
Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa
Nishadi

Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa

2 weeks ago
Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro
Nishadi

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

3 weeks ago
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage
Nishadi

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

3 weeks ago
Next Post
Ko Hana Fina-finan Daba Zai Rage Aikata Laifukan Daba A Kano?

Ko Hana Fina-finan Daba Zai Rage Aikata Laifukan Daba A Kano?

LABARAI MASU NASABA

Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

June 2, 2025
2027: Ƙungiyar Shekarau Ta Gindaya Sharaɗi Kafin Shiga Haɗakar Jam’iyyu

2027: Ƙungiyar Shekarau Ta Gindaya Sharaɗi Kafin Shiga Haɗakar Jam’iyyu

June 2, 2025
Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

June 1, 2025
Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

June 1, 2025
Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara

Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara

June 1, 2025
Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka

Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka

June 1, 2025
Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

June 1, 2025
Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

June 1, 2025
Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

June 1, 2025
bakin wake

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

June 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.