ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Za A Rika Tuna Saratu Gidado Da Su A Fagen Fim

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Saratu

Labarin rasuwar marigayiya Saratu Gidado da ta yi suna a fagen fina-finan Hausa (Kannywood) har ma da wasu na turanci da take yi jefi-jefi, ya yi matukar girgiza ba kawai fage.

Fim ba har da sauran al’umma bisa yadda jarumar ta shahara da kuma irin jin kan da ta fara yi ga al’umma ta gidauniyarta.

  • An Bude Baje Kolin Kayayyakin Masarufi Na Kasa Da Kasa Na Sin Karo Na 4
  • ‘Yan Ta’adda Sun Yi Yunƙurin Ƙwace Iko Da Sakatariyar Jihar Oyo

Ita dai Saratu Gidado wacce ta rasu ranar Talata 9 ga Afrilun 2024, an haife ta ce a Jihar Gombe, a ranar 17-01-1968. Sannan ta yi karatu tun daga matakin firamare a jihar Kano. Daso, wadda tayi suna wajen fitowa a matsayin “Ba Sani Ba Sabo” a shirye shiryenta, ta kasance abar so a wajen masu kallo saboda yadda take yin abu da gaske kuma babu tsoro a cikin Shirin Fim.

ADVERTISEMENT

Daso ta yi suna ne musamman wajen fitowa a matsayin mara tsoro, masifaffiya, da kuma ba sani ba sabo. Wannan shi ne ya sa ta fita daban a cikin ragowar jarumai mata a masana’antar saboda tana iya fitowa a duk yanayin da ake bukata ta fito musamman a matsayin uwa mai tsoratarwa.

Marigayiyar dai ta kasance sananniya a idon duk wani wanda yake Kallon fina-finan Hausa da ma wanda ba ya kallo saboda irin rawar da take takawa sannan kuma ta kasance mace tilo a masana’antar da idan ana bukatar salo na fitowa a uwa ko mace mara kirki ko mara tsoro ko mara tausayi ita ce kadai za ta iya fitowa ta bayar da abinda ake bukata.

LABARAI MASU NASABA

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

Ya Kamata Mawaƙa Su Guji Munafunci Da Hassada Su Rungumi Juna —Fati UK

Har ila yau, ta kasance abar soyuwa a zukatan masu kallo saboda duk da irin ba sani ba sabo da take nunawa amma tana da faran-faran da mutane domin an yi mata shaidar cewa mutuniyar kirki ce.

A shekara ta 2000 ta tsunduma harkokin fina finan hausa, inda ta fara fitowa a cikin Shirin “Linzami Da Wuta” wanda kamfanin Sarauniya ya shirya. Wasu daga cikin fina-finan da ta fito sun hada da ‘Yar Mai Ganye da Nagari da Sansani da Mashi da Fil’azal da Jakar Magori da Gidan Iko da Gidauniya da Uwar Kudi da Gani Ga Ka da kuma Shirin turanci na “There is Way” da kamfanin Jammaje ya shirya.

Shiri na kwana kwanan nan da ya sake fitowa da ita shi ne Shirin LABARINA na kamfanin Saira Mobies, domin an yaba irin rawar da ta taka kuma. A shekara ta 2016 ne Sarkin Kano na 14 Muhammad Sanusi II ya nada ta a matsayin Jakadiya.

Ta kasance mai son taimakawa marayu wajen samar musu abinci da kayan sakawa sannan tana yawan bayyana a shafukan sada zumunta inda take bayyana ra’ayinta a kan abubuwan da ake tattaunawa sannan kuma tana da wata gidauniya ta tallafawa marasa galihu inda ko a cikin watan Ramadana da ya wuce ta rarraba kayan abinci ga marayu da mabukata.

Masu sharhi a kan harkokin fina-finan Hausa dai sun bayyana irin rawar da Daso take takawa a matsayin ta musamman saboda har kawo yanzu babu wata mace da ta taso wadda ake ganin za ta iya maye gurbinta kuma hakan ne ya sa dole idan ana bukatar salo irin nata ita kadai ake iya nema.

Kamar yadda iyalai da ‘yan uwanta suka bayyana, ta rasu da safiyar Talata 9-04-2024  bayan ta dauki azumi na 30, kuma tuni aka yi mata sallah kamar yadda addinin musulunci ya tanada.

Saratu
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?

MASU ALAKA

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro
Nishadi

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Nishadi

Ya Kamata Mawaƙa Su Guji Munafunci Da Hassada Su Rungumi Juna —Fati UK

May 23, 2026
Har Yanzu Burina Bai Cika Ba A Waka —Hadiza Maikano
Nishadi

Har Yanzu Burina Bai Cika Ba A Waka —Hadiza Maikano

May 16, 2026
Next Post
Ko Hana Fina-finan Daba Zai Rage Aikata Laifukan Daba A Kano?

Ko Hana Fina-finan Daba Zai Rage Aikata Laifukan Daba A Kano?

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.