• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Aisha Buhari Za Ta Jagoranci Matan Gwamnoni A Fagen Yaki Da Cin Zarafin Mata

by Bello Hamza
2 years ago
in Labarai
0
Aisha Buhari Za Ta Jagoranci Matan Gwamnoni A Fagen Yaki Da Cin Zarafin Mata
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Uwargidan Shugaban Kasa, Aisha Buhari ta bayyana cewa, za a iya kawo karshen cin zarafin da ake yi wa mata da kananan yara a sassan kasar nan duk kuwa da yadda ake samun karuwar lamarin a ‘yan shekarun nan.

Aisha Buhari ta sanar da haka ne taron kungiyar matan gwamnonin Nijeriya karo na 3 a garin Abuja kwanakin baya, taron mai taken, “Fadakar da al’umma a kan dokar ta-baci a kan cin zarafin mata’.

  • Matan Tubabbun ‘Yan Boko Haram Sun Haifi Jarirai 262 A Wata 4 Kacal

Ta kuma bukkaci kungiyar ta tabbatar da dorewar gangamin musamman ganin a halin yanzu an samu nasarar zartar da dokar kariya ga mata da kananan yara a jihohi 34 na tarrayar Nijeriya.

Uwargidan Shugaban kasar wadda ta samu wakilcin mataimakiyarta ta musamman a kan harkokin mata, Rukayyatu Abdulkareem Gurin, ta kara da cewa, lamarin cinzarafin mata na daya daga cikin abubuwan da aka tattauna a taron kwanaki 16 da aka yi inda waklilai daga kasashen duniya suka samu halarta, musamman ganin mastala ce da ake fama da ita a sassan duniya.

Ta yaba wa matan gwamnonin a kan yadda suka hada kai don ganin an samar da yanayi na kare mata da kananan yara daga cutarwa ta kowacce fuska.

Labarai Masu Nasaba

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

GORON JUMA’A 09/05/2025

Ta ce, “Hanyar samar da daidato da hanyoyin samun aiki ga mata na da matukar muhimmanci, Nijeriya ta yi gaggarumar nasara a wannan fannin, musamman in aka lura da yadda aka zartar da dokar haramta cin zarafin mata ‘ Biolence Against Persons Prohibition (BAPP)’ a wasu jihohi 34 na tarrayar kasar nan.

Ta kuma kara da cewa, kungiyar matan gwamnonin sun kudurin aniyar aiki tare da dukkan masu ruwa da tsaki doin ganin an rage yadda ake cin zarafin mata da kananan yara a kasar nan.

“Yakamata mu kuduri aniyar tabbatar da ganin kowacce mace ko yarinya ta samu ‘yancin rayuwa tare da cikakken kariya daga dukkan abin da zai iya cutar da ita,” in ji ta.
Ana shi jawabin, Shugaban Kungiyar Gwamnonin Nijeriya, kuma Gwamnan Jihar Sakkwato, Aminu Tambuwal, ya tabbatar wa da mata cewa, gwamnoni za su cigaba da bayar da gudummawar da ta kamata don ganin an kawo karshen cin zarafin mata a Nijeriya.

Ya kuma bayar da tabbacin cewa, saura jihohi 2 da basu sanya hannu a kan dokar kariya ga mata ba za su sa hannu nan ba da dadewa ba, ya kuma yaba wa matan gwamnonin a kan wannan kokarin, da yaba masu a kan yadda suka samar da yanayin shirin zai cigaba koda a bayansu ne.

Tunda farko, shugabar kungiyar na matan gwamnonin Nijeriya kuma uwargidan Gwamnan Jihar Sakkwato, Hajiya Mariya Aminu Tambuwal, ta ce, cikin makasudin kafa kungiyar sun hada da tattara masu ruwa da tsaki don ganin an fuskanci matsalar cin zarafin mata a Nijeriya.

Ita a nata jawabin, Ministar Harkokin Mata, Pauline Tallen, ta yaba wa Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai a kan dokoki masu tsauri ga masu cin zarafin mata a jihar, a dokar wanda aka sanya wa hannu a watan Satumba 2021, an tanadi yin dandake ga wadanda aka samu da cin zarafin mata.

Dokar da aka yi wa kwaskwarima ta tanadi duk wani magidanci da aka kama ya yi wa yarinya ko yaro da shekarunsa suke kasa da 14 fyade a yi masa dandaka yayin da macen da aka kama ta yi wa ‘yan yara fyade ita ma za a cire mata mahaifa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Daba Sun Tarwatsa Taron APC, Sun Yi Awon Gaba Da Shugaban Matasa A Delta

Next Post

Ana Sa Ran Cop15 Zai Kai Ga Wani Sabon Matsayi Bayan Yarjejeniyar Paris

Related

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje
Labarai

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

26 minutes ago
GORON JUMA’A 09/05/2025
Labarai

GORON JUMA’A 09/05/2025

1 hour ago
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 
Labarai

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

2 hours ago
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci
Addini

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

3 hours ago
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote
Labarai

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

4 hours ago
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
Manyan Labarai

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

5 hours ago
Next Post
Ana Sa Ran Cop15 Zai Kai Ga Wani Sabon Matsayi Bayan Yarjejeniyar Paris

Ana Sa Ran Cop15 Zai Kai Ga Wani Sabon Matsayi Bayan Yarjejeniyar Paris

LABARAI MASU NASABA

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

May 9, 2025
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.