• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Aisha Buhari Za Ta Jagoranci Matan Gwamnoni A Fagen Yaki Da Cin Zarafin Mata

by Bello Hamza
3 years ago
in Labarai
0
Aisha Buhari Za Ta Jagoranci Matan Gwamnoni A Fagen Yaki Da Cin Zarafin Mata
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Uwargidan Shugaban Kasa, Aisha Buhari ta bayyana cewa, za a iya kawo karshen cin zarafin da ake yi wa mata da kananan yara a sassan kasar nan duk kuwa da yadda ake samun karuwar lamarin a ‘yan shekarun nan.

Aisha Buhari ta sanar da haka ne taron kungiyar matan gwamnonin Nijeriya karo na 3 a garin Abuja kwanakin baya, taron mai taken, “Fadakar da al’umma a kan dokar ta-baci a kan cin zarafin mata’.

  • Matan Tubabbun ‘Yan Boko Haram Sun Haifi Jarirai 262 A Wata 4 Kacal

Ta kuma bukkaci kungiyar ta tabbatar da dorewar gangamin musamman ganin a halin yanzu an samu nasarar zartar da dokar kariya ga mata da kananan yara a jihohi 34 na tarrayar Nijeriya.

Uwargidan Shugaban kasar wadda ta samu wakilcin mataimakiyarta ta musamman a kan harkokin mata, Rukayyatu Abdulkareem Gurin, ta kara da cewa, lamarin cinzarafin mata na daya daga cikin abubuwan da aka tattauna a taron kwanaki 16 da aka yi inda waklilai daga kasashen duniya suka samu halarta, musamman ganin mastala ce da ake fama da ita a sassan duniya.

Ta yaba wa matan gwamnonin a kan yadda suka hada kai don ganin an samar da yanayi na kare mata da kananan yara daga cutarwa ta kowacce fuska.

Labarai Masu Nasaba

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

Ta ce, “Hanyar samar da daidato da hanyoyin samun aiki ga mata na da matukar muhimmanci, Nijeriya ta yi gaggarumar nasara a wannan fannin, musamman in aka lura da yadda aka zartar da dokar haramta cin zarafin mata ‘ Biolence Against Persons Prohibition (BAPP)’ a wasu jihohi 34 na tarrayar kasar nan.

Ta kuma kara da cewa, kungiyar matan gwamnonin sun kudurin aniyar aiki tare da dukkan masu ruwa da tsaki doin ganin an rage yadda ake cin zarafin mata da kananan yara a kasar nan.

“Yakamata mu kuduri aniyar tabbatar da ganin kowacce mace ko yarinya ta samu ‘yancin rayuwa tare da cikakken kariya daga dukkan abin da zai iya cutar da ita,” in ji ta.
Ana shi jawabin, Shugaban Kungiyar Gwamnonin Nijeriya, kuma Gwamnan Jihar Sakkwato, Aminu Tambuwal, ya tabbatar wa da mata cewa, gwamnoni za su cigaba da bayar da gudummawar da ta kamata don ganin an kawo karshen cin zarafin mata a Nijeriya.

Ya kuma bayar da tabbacin cewa, saura jihohi 2 da basu sanya hannu a kan dokar kariya ga mata ba za su sa hannu nan ba da dadewa ba, ya kuma yaba wa matan gwamnonin a kan wannan kokarin, da yaba masu a kan yadda suka samar da yanayin shirin zai cigaba koda a bayansu ne.

Tunda farko, shugabar kungiyar na matan gwamnonin Nijeriya kuma uwargidan Gwamnan Jihar Sakkwato, Hajiya Mariya Aminu Tambuwal, ta ce, cikin makasudin kafa kungiyar sun hada da tattara masu ruwa da tsaki don ganin an fuskanci matsalar cin zarafin mata a Nijeriya.

Ita a nata jawabin, Ministar Harkokin Mata, Pauline Tallen, ta yaba wa Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai a kan dokoki masu tsauri ga masu cin zarafin mata a jihar, a dokar wanda aka sanya wa hannu a watan Satumba 2021, an tanadi yin dandake ga wadanda aka samu da cin zarafin mata.

Dokar da aka yi wa kwaskwarima ta tanadi duk wani magidanci da aka kama ya yi wa yarinya ko yaro da shekarunsa suke kasa da 14 fyade a yi masa dandaka yayin da macen da aka kama ta yi wa ‘yan yara fyade ita ma za a cire mata mahaifa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Daba Sun Tarwatsa Taron APC, Sun Yi Awon Gaba Da Shugaban Matasa A Delta

Next Post

Ana Sa Ran Cop15 Zai Kai Ga Wani Sabon Matsayi Bayan Yarjejeniyar Paris

Related

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka
Ra'ayi Riga

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

9 minutes ago
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya
Rahotonni

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

2 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

11 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

12 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

13 hours ago
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya
Labarai

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

14 hours ago
Next Post
Ana Sa Ran Cop15 Zai Kai Ga Wani Sabon Matsayi Bayan Yarjejeniyar Paris

Ana Sa Ran Cop15 Zai Kai Ga Wani Sabon Matsayi Bayan Yarjejeniyar Paris

LABARAI MASU NASABA

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

August 26, 2025
Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

August 26, 2025
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

August 26, 2025
An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.