• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

by Rabi'u Ali Indabawa
5 seconds ago
in Manyan Labarai
0
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Wakilai Ta Ƙasa (NASS) ta yi gargaɗin cewa idan ba a yi taka tsantsan ba, matsayinta na bashin gwamnati, wanda ya kai Naira tiriliyan 149.39  daidai da Dala biliyan (97) a kwata na farko na shekarar 2025, na iya haifar da haɗari ga makomar ƙasa.

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, da Shugaban Majalisar Wakilai, Hon. Abbas Tajudeen, ne suka yi wannan gargaɗin a taron shekara-shekara na 11 a babban taro na Ƙungiyar Kwamitocin Binciken Asusun Jama’a ta Yammacin Afirka (West Africa Association of Public Accounts Committees – WAAPAC) da aka gudanar a Abuja jiya.

  • Akpabio Ya Ƙaryata Jita-jitar Ba Shi Da Lafiya
  • Kotu Ta Yi Watsi Da Buƙatun Akpabio Kan Dakatar Da Sanata Natasha

Taron shekara-shekara an shirya shi ne ta Kwamitin Kula da Asusun Gwamnati na Majalisar Wakilai, mai taken: “Ƙarfafa Kula da Majalisa kan Bashin Gwamnati.”

Akpabio, wanda Sanata Osita Izunaso, shugaban Kwamitin Kasuwar Hannayen Jari na Majalisar Dattawa ya wakilta, ya bayyana cewa rashin kulawa da bashin gwamnati na iya sanya makomar ‘yan ƙasa cikin haɗari kuma ya raunana dimokuradiyya a faɗin yammacin Afirka.

Ya bayyana cewa kulawar majalisa ba za ta yi watsi da lamarin wajen tabbatar da daidaiton kuɗaɗen gwamnati ba, kuma idan aka sarrafa bashin yadda ya kamata, zai zama muhimmin aiki wajen ɗaukar nauyin ayyukan more rayuwa, da ci gaban ɗorewa.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

Akpabio ya yi kira ga duk ƙasashen membobin WAAPAC da su samar da izinin majalisa ga kwamitocin da suka dace, yana mai cewa hakan zai tabbatar da ‘yancinsu da ingancinsu wajen kare dukiyar jama’a.

“Bashin gwamnati, idan aka sarrafa shi yadda ya kamata, zai zama aiki ne mai muhimmanci wajen ɗaukar nauyin ci gaba, ayyukan more rayuwa, da ci gaba mai ɗorewa. Amma idan aka bar shi ba tare da sanya ido ba aka ɓoye shi cikin rashin gaskiya, zai zama nauyi da ke sanya makomar ‘yan ƙasa cikin haɗari.

Wannan shi ya sa majalisa ba za yi watsi da sanya ido a kansa wajen bashi kulawa ba.

“Kwarewar Nijeriya ta nuna cewa idan kwamitocin majalisa suka samu ikon doka, gaskiya da riƙon amana sun ƙaru, kuɗi ya yi ƙarfi, to dimokuraɗiyya ta ƙara inganci,” in ji shi.

A nasa ɓangaren, Abbas ya gargaɗi cewa basussukan Nijeriya sun kai wani matsayi mai hatsari, inda ya buƙaci majalisun dokoki a faɗin Yammacin Afirka su ƙarfafa sa ido kan aro na gwamnati domin kare makomar ‘yan ƙasashensu.

Da yake magana a madadinsa, Jagoran Majalisar Wakilai, Hon. Julius Ihonɓbhere, Abbas ya bayyana cewa jimillar basussukan gwamnatin Nijeriya ya kai Naira tiriliyan 149.39 (kimanin Dalar Amurka biliyan 97) a zangon farko na shekarar 2025, wanda ya nuna ƙaruwar ta yi tsanani daga Naira tiriliyan 121.7 a shekarar da ta gabata.

Ya bayyana damuwa kan matsayin bashin da aka kwatanta da GDP, wanda a halin yanzu ya kai kusan kashi 52 cikin 100, sama da iyakar kashi 40 cikin 100 da doka ta ƙayyade.

Ya ce: “Wannan karya haddin bashi ne luma hakan wata alama ce ta matsin lamba ga ɗorewar tattalin arziki. Hakan ya nuna gaggawar buƙatar ƙarfafa sa ido, yin aro cikin gaskiya da bayyana dukkan bayanai, da kuma samun haɗin kai domin tabbatar da cewa kowace Naira da aka aro ta samar da ainihin amfanin tattalin arziki da zamantakewa.

“A duk faɗin Afirka, matakin bashi ya kai wani mummunan matsayi. A shekarar 2022, jimillar bashin ƙasashen nahiyar ya kai Dala tiriliyan 1.8, inda bashin wajen shi kaɗai ake sa ran zai zarce Dala tiriliyan 1 a shekarar 2023.”

Ya ce: “Ƙasashe da dama yanzu suna cikin mummunan yanayi na cin bashin da aka kwatanta da GDP: misali; Sudan na da kaso 344, Angola kaso 136.8, Ghana 84, Kenya kusan 70, yayin da Afirka ta Kudu ta haura kaso 77.”

Kakakin majalisar ya lura cewa a faɗin Afirka, bashi ya zama matsalar tsarin tattalin arziki, inda ƙasashe da dama ke kashe kuɗi fiye da na kula da lafiya da sauran muhimman ayyuka wajen biyan bashin da suka karɓa.

A cewarsa, kashi 35 na bashin na ƙasashen Turai ne na masu ba da rance masu zaman kansu, kashi 39 na ƙungiyoyin haɗin gwiwa irin su IMF da Bankin Duniya, kashi 13 kuma na ƙasashen da ke bayar da rance kai tsaye (bilateral creditors), sannan kashi 12 daga Ƙasar China.

Abbas ya ce Nijeriya ta ƙuduri aniyar jagorantar kafa tsarin duba bashin ƙasashen Yammacin Afirka ta majalisar dokoki ƙarƙashin WAAPAC, domin daidaita rahotannin bashi, samar da ƙa’idojin yanki kan gaskiya da bayyana bayanai, tare da bai wa majalisu damar samun bayanai cikin lokaci don inganta bincike.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbbasAkpabio
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Related

‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

2 hours ago
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano
Manyan Labarai

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

5 hours ago
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

6 hours ago
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur
Manyan Labarai

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

6 hours ago
Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya
Manyan Labarai

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

7 hours ago
Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL
Manyan Labarai

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

9 hours ago

LABARAI MASU NASABA

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya

Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya

September 12, 2025
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

September 12, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

September 12, 2025
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

September 12, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

September 12, 2025
Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.