• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Arzikin Duniya Da Na Lahira A Harkar Fim- Malam Inuwa

by Rabilu Sanusi Bena and Sulaiman
9 months ago
Malam Inuwa

Malam Inuwa, daya ne daga cikin dattawa a Masana’antar Kannywood, wanda ya ce, ya fara harkar wasan kwaikwayo, tun kafin zuwan masana’antar ta Kannywood.

Har ila yau, ya bayyana yadda rawa ta canza da kuma yadda shi kansa kidan ya canza a wannan masana’anta, wanda ya bayyana cewa; yanzu ne take cike da mutanen arziki da ke samun arzikin duniya da kuma na lahira, ba kamar a lokacin baya ba.

  • A Shirye Nake Na Tattauna Da Shugaban Rasha – Zelensky
  • An Kaddamar Da Cibiyar Ilimin Fasahar Zamani Ta Sin Da Afirka A Jami’ar Kenya

Inuwa, a wata tattaunawa da ya yi da jaruma Hadiza Gabon, a cikin shirinta na ‘Gabon’s Room Talk Show’, ya bayyana yadda tun kafin zuwan kaset ya fara wannan harka, inda ya ce; a lokacin baya kusan shekara 40 da suka wuce, suna aiki da wata kyamara wadda ke makale da injinta da ake dorawa a kafada a rike abin daukar hoto a hannu, tana da wani kaset na bidiyo da ake kira ‘Betamad’.

A wancan zamanin, idan muka kammala shirin fim; yawo muke gida-gida, musamman ga wadanda muka san cewa; suna da abin kallo a gidajensu, sai mu rika hada su da Allah su karbi kaset din su je su kalla. Haka mu ka yi ta wahala, har Allah ya kawo mu wannan lokaci da muke yanzu.

Malam ya ci gaba da cewa, a wancan lokacin daga cikin jaruman da ake amfani da su wajen shirya fina-finai, akwai mata masu zaman kansu, haka za ka tafi ka jira su gama abin da suke yi; sannan ka tawo da su wajen da ake shirya fim su yi maka aiki ka biya su, ba kamar yanzu da matasa maza da mata masu mutunci, wadanda ke neman halaliyarsu; suka cika masana’antar ba.

LABARAI MASU NASABA

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

Gwarzon Mawaƙin Shekarar 2025, Skales

A zamanin baya, duk da cewa fina-finan nanaye sun fi karbuwa a wajen mutane, amma haka muke kokartawa wajen ganin an shigar da wata koyarwa ta addinin musulinci ko kuma wani abu mai amfani da zai amfanar da al’umma ta wani bangare, amma yanzu duk an daina wannan, masu shirya fina-finai na amfani da labarai masu tsafta da amfanarwa, ba tare da da sanya wakoki ko makamantansu a ciki ba, in ji Malam.

“Dalili kuwa shi ne, yanzu ‘ya’yan mutunci da arziki su ne ke yin harkar, sannan kuma su ne suke samun arzikin duniya da na lahira, akwai lokacin da har mata masu zaman kansu din, sai da muka daina samun su idan zamu yi fim, amma yanzu wannan duk ya zama tarihi”, in ji shi.

Game da tambayar da aka yi masa a kan yadda mutane ke kallon sa, duba da cewa; shi malami ne na addinin musulinci, kuma jarumi a Masana’antar Kannywood cewa ya yi, mutane na yi masa kallon wani Waliyyi a cikinsu, duba da yadda yake isar da sako ko warware wasu matsaloli na musulunci da suka shige wa al’umma duhu ta hanyar fim.

Dangane da yadda yake kallon tarbiyar jaruman Kannywood na yanzu maza da mata, Malam ya sake jaddada maganarsa ta cewa; mutanen kirki ne matuka, sannan akwai wasu maganganu da wasu jahilai wadanda ake yi wa kallon malamai suke yi dangane da jaruman wannan masana’anta ta Kannywood, domin idan har wani zai yanke hukunci a kan tarbiyar jaruman Kannywood, to ba zai wuce mu da muke tare da su ba.

Sannan kuma, duk duniya babu wani jarumin fim mutumin kirki irin dan Masana’antar Kannywood, domin kuwa shi kadai ne yake yin fina-finansa da sauran al’amuran rayuwa a gaban jama’a kowa yana gani, ba tare da ya saka wani hijabi ba, sannan dan Kannywood; ba ya ashariya, ba a hada jiki tsakanin mace da namij, ballantana har ta kai ga sumbata kamar yadda muke gani ana yi a wasu masana’antun shirya fina-finai a sauran sassan duniya.

Daga karshe, ya bayyana cewa; dukkannin wani malami da ma wanda ba malami ba, ya sani duk lokacin da ka bayyana wani abu marar kyawu da wani ya yi a boye ko da yana yi, amma sai ya boye yayin da zai aikata wannan abu, to ka sani Manzon Allah SAW ya ce, ba za ka mutu ba sai ka aikata wannan abu da ka ce yana yi, ko da kuwa yana yi din.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
Nishadi

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Mawaƙin Shekarar 2025, Skales

October 25, 2025
Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 
Nishadi

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

October 11, 2025
Next Post
‘Yan Asalin Nijeriya Da Ke Buga Wa Kasashen Turai Wasa

'Yan Asalin Nijeriya Da Ke Buga Wa Kasashen Turai Wasa

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025
Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

November 5, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 5, 2025
Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

November 5, 2025
Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.