ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Arzikin Duniya Da Na Lahira A Harkar Fim- Malam Inuwa

by Rabilu Sanusi Bena and Sulaiman
2 years ago
Malam Inuwa

Malam Inuwa, daya ne daga cikin dattawa a Masana’antar Kannywood, wanda ya ce, ya fara harkar wasan kwaikwayo, tun kafin zuwan masana’antar ta Kannywood.

Har ila yau, ya bayyana yadda rawa ta canza da kuma yadda shi kansa kidan ya canza a wannan masana’anta, wanda ya bayyana cewa; yanzu ne take cike da mutanen arziki da ke samun arzikin duniya da kuma na lahira, ba kamar a lokacin baya ba.

  • A Shirye Nake Na Tattauna Da Shugaban Rasha – Zelensky
  • An Kaddamar Da Cibiyar Ilimin Fasahar Zamani Ta Sin Da Afirka A Jami’ar Kenya

Inuwa, a wata tattaunawa da ya yi da jaruma Hadiza Gabon, a cikin shirinta na ‘Gabon’s Room Talk Show’, ya bayyana yadda tun kafin zuwan kaset ya fara wannan harka, inda ya ce; a lokacin baya kusan shekara 40 da suka wuce, suna aiki da wata kyamara wadda ke makale da injinta da ake dorawa a kafada a rike abin daukar hoto a hannu, tana da wani kaset na bidiyo da ake kira ‘Betamad’.

ADVERTISEMENT

A wancan zamanin, idan muka kammala shirin fim; yawo muke gida-gida, musamman ga wadanda muka san cewa; suna da abin kallo a gidajensu, sai mu rika hada su da Allah su karbi kaset din su je su kalla. Haka mu ka yi ta wahala, har Allah ya kawo mu wannan lokaci da muke yanzu.

Malam ya ci gaba da cewa, a wancan lokacin daga cikin jaruman da ake amfani da su wajen shirya fina-finai, akwai mata masu zaman kansu, haka za ka tafi ka jira su gama abin da suke yi; sannan ka tawo da su wajen da ake shirya fim su yi maka aiki ka biya su, ba kamar yanzu da matasa maza da mata masu mutunci, wadanda ke neman halaliyarsu; suka cika masana’antar ba.

LABARAI MASU NASABA

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa

Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

A zamanin baya, duk da cewa fina-finan nanaye sun fi karbuwa a wajen mutane, amma haka muke kokartawa wajen ganin an shigar da wata koyarwa ta addinin musulinci ko kuma wani abu mai amfani da zai amfanar da al’umma ta wani bangare, amma yanzu duk an daina wannan, masu shirya fina-finai na amfani da labarai masu tsafta da amfanarwa, ba tare da da sanya wakoki ko makamantansu a ciki ba, in ji Malam.

“Dalili kuwa shi ne, yanzu ‘ya’yan mutunci da arziki su ne ke yin harkar, sannan kuma su ne suke samun arzikin duniya da na lahira, akwai lokacin da har mata masu zaman kansu din, sai da muka daina samun su idan zamu yi fim, amma yanzu wannan duk ya zama tarihi”, in ji shi.

Game da tambayar da aka yi masa a kan yadda mutane ke kallon sa, duba da cewa; shi malami ne na addinin musulinci, kuma jarumi a Masana’antar Kannywood cewa ya yi, mutane na yi masa kallon wani Waliyyi a cikinsu, duba da yadda yake isar da sako ko warware wasu matsaloli na musulunci da suka shige wa al’umma duhu ta hanyar fim.

Dangane da yadda yake kallon tarbiyar jaruman Kannywood na yanzu maza da mata, Malam ya sake jaddada maganarsa ta cewa; mutanen kirki ne matuka, sannan akwai wasu maganganu da wasu jahilai wadanda ake yi wa kallon malamai suke yi dangane da jaruman wannan masana’anta ta Kannywood, domin idan har wani zai yanke hukunci a kan tarbiyar jaruman Kannywood, to ba zai wuce mu da muke tare da su ba.

Sannan kuma, duk duniya babu wani jarumin fim mutumin kirki irin dan Masana’antar Kannywood, domin kuwa shi kadai ne yake yin fina-finansa da sauran al’amuran rayuwa a gaban jama’a kowa yana gani, ba tare da ya saka wani hijabi ba, sannan dan Kannywood; ba ya ashariya, ba a hada jiki tsakanin mace da namij, ballantana har ta kai ga sumbata kamar yadda muke gani ana yi a wasu masana’antun shirya fina-finai a sauran sassan duniya.

Daga karshe, ya bayyana cewa; dukkannin wani malami da ma wanda ba malami ba, ya sani duk lokacin da ka bayyana wani abu marar kyawu da wani ya yi a boye ko da yana yi, amma sai ya boye yayin da zai aikata wannan abu, to ka sani Manzon Allah SAW ya ce, ba za ka mutu ba sai ka aikata wannan abu da ka ce yana yi, ko da kuwa yana yi din.

Malam Inuwa
Rabilu Sanusi Bena
+ posts Bio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Za’a Dakatar Da Wasa A Farkon Minti 10 Na Kowane Wasa A Kasar Argentina Saboda Girmama Messi
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Chelsea Ta Kammala Ɗaukar Ahanor Kan Fam Miliyan 40
Malam Inuwa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
Nishadi

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa

September 5, 2026
Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood
Nishadi

Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

August 29, 2026
Malam Inuwa
Nishadi

Dalilan Da Suka Sa Ba Zan Iya Auren Ɗan Film Ba —Bilkisu Bishasha

August 23, 2026
Next Post
‘Yan Asalin Nijeriya Da Ke Buga Wa Kasashen Turai Wasa

'Yan Asalin Nijeriya Da Ke Buga Wa Kasashen Turai Wasa

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.