• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Ma’ana Mai Zurfi A Bayan Da’a

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 month ago
in Ra'ayi Riga
0
Akwai Ma’ana Mai Zurfi A Bayan Da’a
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ranar 25 ga watan Mayu, rana ce ta “Ranar Afirka”, wato ranar tunawa da kafuwar Kungiyar Hadin Kan Afirka, wadda daga bisani ta zama Kungiyar Tarayyar Afirka ta AU. A jiya Litinin, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya gana da daukacin jakadun kasashen Afirka da ke kasar Sin a birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin, inda suka gudanar da bikin murnar wannan rana mai ma’anar musamman ga Afirka. Wannan ya nuna abokantaka da ke tsakanin Sin da Afirka, tare da shaida yadda mutanen Sin da Afirka suke dora muhimmanci kan da’a.

‘Yan Afirka, kamar Sinawa, suna mai da hankali sosai ga da’a. A duk lokacin bukukuwa, na kan samu kiran waya da gaisuwa daga abokai ‘yan Afirka da yawa. Ina ganin za su iya fahimtar muhimmancin bikin da ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya shirya a wannan karo, da sauran abubuwan da suka nuna yadda jama’ar kasar Sin suke daukar da’a da muhimmanci, misalin ziyarar da ministan harkokin wajen kasar Sin ya kan kai Afirka a farkon kowace shekara.

  • Gwamnati Ta Kammala Samar Da Fasfo Sama Da 200,000 Da Suka Yi Jinkiri
  • Tsarin Dunkulewar Aiki Ba Da Ilmi Da Kimiyya Da Kwararru Na Sin Ya Dace Da Yanayin Zamani

Da’a ba ta shafi “al’ada” kawai ba, tana kuma wakiltar ka’idoji da dabi’a, da dorewar huldar mutane da ta kasa da kasa. Kamar dai wannan biki na tunawa da “ranar Afirka”, wanda ya tattaro wakilan Sin da Afirka, don waiwayar yadda jama’ar Sin da ta Afirka suka nuna goyon baya ga juna a fafutukar kare ikon mulkin kasa, da kuma taimakawa juna a kokarin farfado da al’umma, tare da alkawarin ci gaba da kokarin hadin kai a nan gaba. Wannan yanayin hulda mai dorewa yana baiwa mutane damar mai da hankali kan tsare-tsaren ci gaba na dogon lokaci, da kuma neman inganta dangantakar hadin gwiwa tsakanin kasashe a kai a kai. Kasar da ke da da’a da mutunci ba za ta taba kaddamar da yakin haraji kan kasashen duniya ba, saboda ta fahimci darajar kwanciyar hankali da yanayin tabbaci ga ci gaban wata kasa da na al’ummarta cikin dogon lokaci.

 

Da’a da dabi’a sun shafi mutunta juna, wanda shi ne abin da ake bukata don samun sakamako mai gamsarwa ga dukkan bangarorin da suke hadin gwiwa da juna. Saboda tana mutunta kasashen Afirka, kasar Sin ta iya daidaita yadda ake rarraba moriya a hadin gwiwar da ke tsakaninta da Afirka, da kuma ba da karin goyon baya wajen biyan bukatun raya kasashen Afirka. Misali, a shekarar 2024, kayayyakin da kasar Sin ta shigo da su daga Afirka sun karu da kashi 6.9%, wanda ya zarta karuwar kashi 3.5% na kayayyakin da take fitarwa zuwa kasashen Afirka. Ban da haka, yankunan ciniki cikin ‘yanci na Lekki, da na Ogun-Guangdong da kamfanonin kasar Sin suka zuba jari a cikinsu, da gina su, da sarrafa su a Najeriya, sun samar da guraben ayyukan yi sama da 20,000 ga al’ummar Najeriya, tare da jawo jarin kimanin dalar Amurka biliyan 2.6. Wadannan misalan sun nuna irin kokarin da kasar Sin ke yi na inganta hadin gwiwa mai amfanar juna tare da kasashen Afirka. Ba kamar a wata kasa ta daban ba, inda aka tilastawa shugaban wata babbar kasa ta Afirka da ya yi hakuri da tsokana, da wulakanci a gaban daukacin jama’ar duniya baki daya. Irin wannan kasa bata ganin komai sai karfi kadai, tana son cin moriya da faduwar wani, kuma ba ta san da’a da mutunci, da yiwuwar samun ci gaba na bai daya ba.

Labarai Masu Nasaba

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

 

Tabbas a halin yanzu, wasu kasashe ba su ba da’a muhimmanci ba, kana suna ta daukar matakan kashin kai yadda suka ga dama, lamarin da ya sa al’amuran kasa da kasa suka shiga rudani. Dangane da wannan batu, dole ne Sin da kasashen Afirka masu da’a su karfafa hadin kai, su yi adawa da siyasar nuna fin karfi, da daukaka ra’ayin cudanyar mabambantan bangarori masu fada-a-ji a duniya, da kare tsarin kasa da kasa dake karkashin jagorancin Majalisar Dinkin Duniya. Ta la’akari da yadda adadin yawan al’ummar Sin da Afirka ya kai kashi daya bisa uku na yawan al’ummar duniya, kokarin hadin gwiwarmu tabbas zai karkata duniya zuwa ga turba mai dacewa. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaba Tinubu Ya Amince Da Ɗaga Likafar Kwalejin Fasaha Ta Kabo Zuwa Jami’a

Next Post

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Amso Bashin $21.5bn Da ₦757.9bn

Related

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

21 hours ago
Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa
Ra'ayi Riga

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

2 days ago
Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya
Ra'ayi Riga

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

7 days ago
Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa
Ra'ayi Riga

Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

1 week ago
Kayan Aro Baya Rufe Katara
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa JKS Mai Tsawon Tarihin Sama Da Shekaru 100 Ta Dore A Kan Mulki

1 week ago
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…
Ra'ayi Riga

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

2 weeks ago
Next Post
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Amso Bashin $21.5bn Da ₦757.9bn

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Zamfara Ya Raba Buhunan Taki 59,205 Ga Manoman Jihar

Gwamnan Zamfara Ya Raba Buhunan Taki 59,205 Ga Manoman Jihar

July 11, 2025
Matatun Man Fetur Na Nijeriya Ba Za Su Ci Gaba Da Aiki Yadda Ya Kamata Ba – Dangote

Matatun Man Fetur Na Nijeriya Ba Za Su Ci Gaba Da Aiki Yadda Ya Kamata Ba – Dangote

July 11, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa ‘Yansanda Hari Tare Da Kashe Wani Mutum Da Raunata Wani A Nasarawa

July 11, 2025
Goron Sallah

GORON JUMA’A

July 11, 2025
An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

July 11, 2025
Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

July 11, 2025
Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

July 11, 2025
NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

July 11, 2025
Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

July 11, 2025
NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.