Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home KASUWANCI

Akwai Tagomashi A Sana’ar Siyar Da Magunguna

by Tayo Adelaja
September 25, 2017
in KASUWANCI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Muhammad Sani Chinade, Damaturu

LEADERSHIP A Yau ta samu tattaunawa da wani matashi dan kimanin shekara 26 da ke sana’ar sayar da magungunan zamani Yusuf Muhammad Lamsha Potaskum a Jihar Yobe wanda a yanzu haka ya mallaki kantunan sayar da magunguna na zamani Kemis guda biyu wadanda ya ce, sana’ar sayar da magungunan zamani ta yi masa komai na rayuwa.

LEADERSHIP A YAU: Yaushe ka fara gudanar da wannan sana’a taka ta sayar da magungunan zamani (medicine), kuma ta yaya ka fara?

LAMSHA: To alhamdu lillah na fara sana’ar sayar da magungunan zamani ne tun a shekarar 2005 wato tun ina dan shekara 15 ke nan kuma na fara ne da kasa magungunan a cikin kwando ina yawo kwararo-kwararo daga bisani kuma na fara zuwa kasuwanni.

Malam Yusuf, ya kara da cewa, bayan da ya ga abubuwan sun fara bunkasa sai ya zauna wuri guda tare da wani maigidansa Dr Muhammad mai medicine a cikin tashar motar Potaskum yadda daga baya ya bude dan wani karamin shago ya zuba magungunan yana sayarwa ciki. Ya ci gaba da cewa, yana hakan ne sai Allah (SWT) Ya masa nasibi jarinsa ya ci gaba da bunkasa ta yadda ya fita wajen tashar ya sayi wani shago ya zuba magunguna a matsayin kantin sayar da magani kemis ta yadda a duk sati sai ya je Kano don sayo  magunguna yana rarrabawa wadanda ya ke hulda da su. Ana cikin hakan kuma ya kara sayen wani shagon na biyu a cikin tsohuwar tasha ya sake zuba magunguna, abin sai san barka.

LEADERSHIP A YAU: Bayan kantuna biyu da ka bude, shin ko akwai wasu karin nasarori da ka cimma da kake fahari da su a kan wannan sana’a?

LAMSHA:.Alal hakika na cimma karin nasarori na rayuwa da nake fahari da su dangane da wannan sana’a ta sayar da magunguna, domin bayan shagunguna biyu da na bude cike da magunguna na kuma gina gidan kaina na yi aure na sa amaryar ciki kana nakan dduki kusan dukannin dawainiyar iyalen gidanmu tare da biyan kudaden makarantar kannena kuma ni kaina ma na dauki dawainiyar kaina da kaina yadda har na je na yi karatun Diploma da ta yi sanadiyar samun aikin gwamnati da sauran dawainiya ta ‘yan’uwa da abokan arziki  daidai gwargwadon yadda zan iya. Don haka a gaskiya wannan sana’a ta sayar da magungunan zamani ta yi min komai na rayuwa tabarkallah.

LEADERSHIP A YAU: Da yake wannan irin sana’a taku na bukatar kwarewa da neman izini daga hukuma, shin ko kaima ka bi wannan mataki?

LAMSHA…Alal hakika hukuma ta san da ni don kuma na samu izinin bude kantunan sayar da magani daga gare ta. Kuma batun kwarewa kuwa alhamdu lillah ina da daidai gwargwado.

LEADERSHIP A YAU…Wane kira kake da shi ga  masu wannan irin wannan sana’a taka ta sayar da magunguna musamman don bin doka da oda?

LAMSHA.:To ina kira da babbar murya ga ‘yan’uwana dake wannan sana’a ta sayar da magungunan zamani na gefen tituna da masu zama wuri daya a kantuna da a guji ta’ammali da sayar da miyagun kwayoyin da gwamnati ta hana da kuma kwayoyin da amfaninsu ya kare da wadanda ba su da lambobi da sauransu.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Bunkasar Kasuwar Kwari A Cikin Shekaru 45

Next Post

BANGON FARKO

RelatedPosts

Mun Yaba Da Kokarin Kamfanin Bizi Mobile – Gwamnatin Kano

Mun Yaba Da Kokarin Kamfanin Bizi Mobile – Gwamnatin Kano

by Sulaiman Ibrahim
3 days ago
0

Daga Ibrahim Ibrahim, Kaduna A yunkurinsa na ganin a ko...

Ya Dace Gwamnati Ta Tallafa Wa Masu Sarrafa Tsoffin Robobi – Bala Musa

Ya Dace Gwamnati Ta Tallafa Wa Masu Sarrafa Tsoffin Robobi – Bala Musa

by Sulaiman Ibrahim
3 days ago
0

Daga Sani Tahir Kano Duk wata sana’a tana da matukar...

Kamfanin KEDCO Ya Kaddamar Da Sanya Mita Kyauta Karo Na Biyu A Kebbi

Kamfanin KEDCO Ya Kaddamar Da Sanya Mita Kyauta Karo Na Biyu A Kebbi

by Sulaiman Ibrahim
3 days ago
0

Daga Jamil Gulma Birnin Kebbi Kamfanin samarda wutar lantarki da...

Next Post

BANGON FARKO

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version