• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Alaafin Ya Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Kama Masu Kashe Kashe A Kwara

by Abubakar Sulaiman
3 weeks ago
Tarayya

Alaafin na Oyo, Oba Abimbola Akeem Owoade, ya roƙi gwamnatin tarayya ta matsa ƙaimi wajen ganowa da kuma kama masu hannu a kashe-kashen da suka auku a wasu yankunan Kwara domin fuskantar hukunci. Ya kuma yi kira ga ƴan Nijeriya da su haɗa kai wajen tunkarar waɗanda ya kira “masu shan jinin jama’a”, waɗanda suke jin daɗi da kisan rayukan marasa laifi.

Oba Owoade ya bayyana cewa hukunta waɗannan miyagun zai ƙarfafa haɗin kan al’umma domin kuɓutar da ƙasa daga ƙangin ta’addanci da rashin imani. Ya kuma jaddada cewa dole ne a kiyaye al’adun da ke ɗaukaka girmama rayuwa da mutuncin ɗan Adam, domin kada a miƙa su ga marasa imani.

  • Collins Daga BUK Na Dab Da Shiga Kundin ‘Guinness World Record’ Tare Da Goyon Bayan Indomie
  • Wadanne Kasashen Afirka Ne Ba Sa Goyon Bayan Kafa Kasar Falasdinawa?

Wannan kira na Alaafin ya biyo bayan kashe wasu ƴan ƙabilar Yarbawa da ake zargin makiyaya Fulani ne suka yi a Oke Ode, jihar Kwara. A cikin wata sanarwa da mai taimaka masa wajen hulɗa da manema labarai, Bode Durojaye, ya fitar a ranar Alhamis, an bayyana cewa Sarkin ya riga ya tuntubi gwamnan jihar, AbdulRahman AbdulRasaq, kan wannan mummunan lamari.

A cewar sanarwar, gwamnan ya tabbatar wa da Oba Owoade cewa an tura dakarun tsaro zuwa yankin domin dawo da zaman lafiya da tabbatar da tsaron mazauna yankin. Sarkin ya kuma yi kira ga shugabanni da jama’a gaba ɗaya da su yi gaskiya wajen fuskantar tushen matsalar tsaro da ta ƙunshi aikata laifuka, tayar da ƙayar baya, da kuma ta’addancin makiyaya da ya ƙara tsananta kwanan nan.

Yayin da yake yaba wa hukumomin tsaro bisa jajircewarsu, Alaafin ya yi gargaɗin kauce wa duk wani abu da zai kawo barazana ga zaman lafiya, da daidaito, da haɗin kan ƙasa.

LABARAI MASU NASABA

Thomas Etuh: Gwarzon Ɗan Kasuwa Na 2025

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Thomas Etuh: Gwarzon Ɗan Kasuwa Na 2025

October 25, 2025
Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)
Manyan Labarai

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo): Hiddimta Wa Al’umma Ba Tare Da Gajiyawa Ba

October 25, 2025
Next Post
Kasar Sin Ta Nuna Takaici Da Matakin Amurka Na Kin Amincewa Da Daftarin Kudurin Gaza

Kasar Sin Ta Nuna Takaici Da Matakin Amurka Na Kin Amincewa Da Daftarin Kudurin Gaza

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Thomas Etuh: Gwarzon Ɗan Kasuwa Na 2025

October 25, 2025
Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo): Hiddimta Wa Al’umma Ba Tare Da Gajiyawa Ba

October 25, 2025
Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025
Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 24, 2025

Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci

October 24, 2025
Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

October 24, 2025
Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.