• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Albishir Ga ’Yan Kasuwar Ketare Dake Kasar Sin

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Albishir Ga ’Yan Kasuwar Ketare Dake Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun lokacin da kasar Sin ta sanar da inganta matakanta na yaki da annobar COVID-19, kanana da manyan harkoki na kasuwanci ke kara bunkasa a sassa daban-daban na fadin kasar. Tituna sun kara cika da ababan hawa, wuraren shakatawa da na motsa jiki ma ba a bar su a baya ba.

Ana haka ne kuma, sai hukumomi suka sanar da kaddamar da sauyi a dokar gudanar da rijistar hada-hadar cinikayyar kamfanonin ketare dake cikin kasar, duk da nufin kara bunkasa harkokin kasuwanci a kasar.

  • Jawabin Murnar Shiga Sabuwar Shekara Na Shugaban CMG 

A karkashin wannan sauyi, hukumomin da abun ya shafa, sun dakatar da neman takardun rajistar kasuwancin waje, daga kamfanonin dake hada hadar shige da ficen hajoji, da takardun shaidar rajistar fasaha ta kwangilolin shige da fice, da shaidar kayyade hajoji, da takardun shaidar gudanar da kasuwanci na gwamnati, da ma wasu sauran takardu masu nasaba da hakan. Matakin dake kara tabbatar da alkawarin kasar na kara zurfafa bude kofa.

Ma’aikatar cinikayyar kasar Sin a nata bangare, ta ce wannan sauyi na da matukar muhimmanci ga masu gudanar da harkokin kasuwancin waje dake kasar Sin. Kaza lika sabon salo ne da gwamnatin Sin ta bullo da shi domin bunkasa cinikayya, da sakarwa kasuwa mara.

Masu fashin baki na cewa, matakin zai taimaka wajen kyautata damar gudanar da kasuwanci a saukake, da ingiza damar bunkasa cinikayyar kamfanonin waje, da bunkasa cinikayya mai nagarta, da kara bude kofa bisa matsayin koli.

Labarai Masu Nasaba

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Wani rahoton bincike ya nuna cewa, a cikin ’yan shekarun nan, manyan kamfanonin kera kayayyaki na kasar Sin, sun samu ci gaba matuka, inda kasuwar ta kara samun darajar da ma fadada tasirinta a kasuwannin ketare.

A halin da ake yanzu, yawan kamfanonin kera kayayyaki masu hannun jari dake rukuni na A ko A-share a Turance, ya kai 2,121, wanda ya karu da kashi 69.7 bisa dari daga 1,250 a karshen shekarar 2017. Yayin da darajar manyan kamfanonin kera kayayyaki a kasuwa da aka zayyana, sun karu sosai daga shekarar 2017 zuwa ta 2021. Wadannan kamfanoni sun samu kudin shiga da yawansu ya kai yuan tiriliyan 11.79 kwatankwacin dalar Amurka tiriliyan 1.69, a cikin kudaden shiga na ayyukan da suka gudana a shekarar 2021, idan aka kwatanta da yuan tiriliyan 7.47 a shekarar 2017.

Wannan na kara nuna cewa, manufar kasar Sin ta bude kofa ga kasashen waje na kara amsa sunanta. (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Tana Nacewa Ga Musanyar Bayanai Da Kasashen Ketare Ta Hanyar Da Ta Dace

Next Post

Kotu Ta Dakatar Da DSS Kan Cafke Shugaban Hukumar INEC

Related

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu
Daga Birnin Sin

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

6 hours ago
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili
Daga Birnin Sin

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

8 hours ago
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

8 hours ago
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

12 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

14 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

14 hours ago
Next Post
Kotu Ta Dakatar Da DSS Kan Cafke Shugaban Hukumar INEC

Kotu Ta Dakatar Da DSS Kan Cafke Shugaban Hukumar INEC

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.