• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Alfanun Da Ke Tattare Da Sabon Tsarin Cire Kudi Na CBN – Sanusi

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Alfanun Da Ke Tattare Da Sabon Tsarin Cire Kudi Na CBN – Sanusi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Sanusi Lamido Sanusi ya bayyana cewa sabon tsarin da CBN ya bullo da shi na kayyade cire kudi yana da alfanu mai yawan gaske.

Ya ce tsarin ya dade tun a 2012 lokacion da yake gwamanan babban bankin suka so bullo da shi, ya ce a yanzu CBN ya ci gaba daga inda ya tsaya.

  • Abubuwan Lura Guda 6 Game Da Sabbin Dokokin CBN Na Mu’amalar Kudi

Ya ce, “Tsarin takaita cire kudade ya samo asali ne tun a 2012 lokacin da nake gwamnan CBN, inda aka fara da Jihar Legas sannan ya watsu har zuwa jihohi guda biyar. Bayanan da muka samu a wancen lokaci, duniya tana bunkasa wanda take hana mutane rike tsabar kudi tare da samar da sabon tsarin takaita kudade wajen gudanar da hada-hadar kasuwanci.

“Da farko mutane sun kalubalanci tsarin, amma daga baya sun amince da shi tare da fara yin amfani da mabanbantan tsarin biyan kudade a wuraren cin abinci da shaguna da sauran wurare,” in ji shi.

Ya kara da cewa daya daga cikin muhimmancin dokar kayyade kudade shi ne, zai hana yin magudin siyan kuri’u, sannan ya gargadi ‘yan Nijeriya su manta da ‘yan siyasan da suke korafi kan wannan doka domin su zai fi shafa sakamakon amfani da kudade da suke yi wajen sayan kuri’u.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

“Ina shawartar mutane su kuda da ‘yan siyasan da suke kalubalantar tsarin dokar kayyade cire kudadde, domin su za su fi cutuwa da tsarin. Suna kwashe shekaru hudu a kan mukami ba tare da sun iya sauke nauyin da ya rataya a wuyansu ba, sannan daga baya su riko makudan kudade da suke tunanin za su yi amfani da su wajen bai wa jami’an tsaro da jami’an zabe ci hanci.

“Tsarin zai kuntata wa ‘yan siyasan da ke kokarin bai wa jami’an tsaro da jami’an zabe cin hanci, dole mutum ya saka kudaden a asusunsa na kashin kai wanda kuma za a iya bincikawa. Domin haka, ina kira ga mutane su rungumi tsarin hannu bibbiyu a matsayin hanyar tsaftace dimokuradiyya da kuma hana ‘yan siyasa yin murdiya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hakimi Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Sumbatar Mahaifiyarsa

Next Post

Na Yi Bakin Kokarina A Matsayin Shugaban Nijeriya — Buhari

Related

Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

12 hours ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

1 week ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

2 weeks ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

2 weeks ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

1 month ago
Sanusi
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

1 month ago
Next Post
Buhari Zai Kaddamar Da Sabbin Takardun Kudi A Taron Majalisar Zartwar Ta Kasa Ranar Laraba

Na Yi Bakin Kokarina A Matsayin Shugaban Nijeriya — Buhari

LABARAI MASU NASABA

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Sanusi

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.