Daga Abubakar Abba, Kaduna
Hukumar Alhazai ta jihar Kaduna ta bayyana cewa, Alhazan jihar dubu 2,842 ne suka dawo gida daga kasar Saudiyya.
Kakakin Hukumar Alhazai ta Jihar Kaduna, Yunusa Abdullahi, ya shaidawa wakilinmu hakan ta wayar tarho.
Ya ce, alhazan an dawo da su ne a jirgen ‘Medbiew’ da ‘Mad Air’ a jigila ta shida. Ya kara da cewa, Medbiew ya dawo da Alhazai su 1,786, jirgin Mad Air kuma ya dawo da Alhazai 1,078.