• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Alkawarin Da Tinubu Ya Yi Wa Ma’aikatan Gwamnati

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Alkawarin Da Tinubu Ya Yi Wa Ma’aikatan Gwamnati
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Zababben shugaban kasa, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya bai wa ma’aikata tabba-cin samun kyakykyawan rayuwa a gwamnatinsa.

Ya ce zai ba su fiye da mafi karancin albashi da za su iya gudanar da rayuwarsu da ta iyalansu.

  • Na Gwammace Zama Mashawarci A Gefe, Ba Shugaban Ma’aikatan Tinubu Ba – El-Rufai

Ya kuma yi alkawarin zama amintaccen aminin ma’aikatan kasar nan da zaran an rantsar da gwamnatinsa a ranar 29 ga Mayun 2023.

Wadannan alkawuran na kunshe ne a cikin sakon bikin ranar ma’aikata na wan-nan shikerar da ya sanya wa hannu.

Da yake tabbatar wa ma’aikatan kasar nan ta hannun kungiyar kwadago (NLC) da kuma kungiyar ‘yan kasuwa (TUC), Tinubu cewa “Da zarar an rantsar da shi a ranar 29 ga watan Mayu a matsayin shugaban Nijeriya, ma’aikata za su samu fiye da mafi karancin albashi. Za ku sami albashi fiye da mafi karancin albashi da za ku iya gudanar da rayuwarku da ta iyalanku.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

“A karkashin shugabancina, za ku sami ‘yanci da walwalan aiki wajen yakir rashin adalci na zamantakewa da tattalin arziki ga daukacin ‘yan Nijeriya, gami da duk ma’aikata.

“Yakinku zai zama yakina, saboda a ko da yaushe ni zan muku yaki. Ina da shirye-shiryen inganta walwala da yanayin aiki mai kyau a cikin ajandar gwamnatina, saboda samar da ingantaccen Nijeriya.

Alkawari ne akai na tun lokacin da aka hai-fe nake kokarin yadda za a inganta rayuwar ma’aikata.”

Da yake kiran hadin kan ma’aikata, Tinubu ya shawarce su da cewa, “Kwanaki masu zuwa, ana bukatar fahimtar juna da hadin kai daga kowane bangare, saboda shugabanci na bukaci mu dauki tsauraren matakai domin jama’armu da ma’aikatan Nijeriya su samu rayuwa mai inganci.”

Zababben shugaban kasar ya nemi goyon daukacin ma’aikatan Nijeriya, inda ya nemi ma’aikata da su hada kai da gwamnatinsa mai jiran gado wajen yakir fatara, jahilci, cututtuka, rashin hadin kai, kabilanci da mambancin addini da duk wani mummunan lamari da ka iya barazana ga zaman lafiya da hadin kan kasa.

Tinubu ya yaba da irin rawar da ma’aikatan Nijeriya suke takawa wajen gina kasa.
Ya ce, “Na bi sahun sauran kasashen duniya da sauran ‘yan’uwa domin murnar ranar ma’aikata ta duniya ta bana. Yau rana ce ta musamman a mafi yawan kasashen duniya, rana ce ta gaisuwa da karrama ma’aikatan da kwazonsu da guminsu ke ci gaba da rura wutar ci gaban Bil’adama.

“Wannan rana tana da matukar mahimmanci ta fuskoki da yawa. Rana ce da aka kirkira saboda gwagwarmayar neman hakkin ma’aikata da ‘yancinsu na zaman-takewa da tattalin arziki. Tun daga shekara ta 1891, aka fara bikin wannan rana a duk fadin duniya.

“A Nijeriya, kowace ranar 1 ga Mayu rana ce ta musamman a kalandar kasarmu. Ranar hutu ce ga al’umma da muke yi ba wai don tunawa da gudunmawa da sa-daukarwar da ma’aikata suke bayarwa ba ne don ci gaban kasarmu ce.

Ta kasance ranar bikin hakkin ma’aikata da kare mutuncisu da ingantaccen albashi da rayuwa mai kyau, kuma mafi mahimmanci shi ne, muhimmiyar rawar da kungiyar kwadago ke takawa wajen hadin kan kasarmu.

“Tun a shekarar 1945 lokacin da ma’aikatan jirgin kasa da wasu kungiyoyin ma’aikatan gwamnati 16 suka jagoranci yajin aikin farko na neman karin albashi sakamakon tsadar rayuwa, kungiyar kwadago a Nijeriya a ko da yaushe tana yaki domin talakawan kasarmu.

Ba abin mamaki ba ne cewa kungiyar ta kara kuzari ga gwagwarmayar neman ‘yancin kai ta hanyar hada kai da masu kishin kasa irin su Nnamdi Azikiwe, Herbert Macaulay, Ahmadu Bello, Obafemi Awolowo, Ernest Ikoli da Anthony Enahoro da sauransu.

“Haka kuma an samu kungiyar kwadago a Nijeriya ne a daidai lokacin da muke gwagwarmayar maido da mulkin dimokuradiyya. Kungiyar kwadago ta Nijeriya da kungiyoyin da ke da alaka da ita kamar irin su NUPENG, Tedtile, PENGASSAN, da dai sauransu, sun hada kai da shugabanni da kungiyoyi masu fafutukar tabba-tar da dimokuradiyya wajen maido da mulkin dimokuradiyya a Nijeriya a shekarar 1999 bayan kusan shekaru biyu na mulkin kama-karya na sojoji.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘YarAdua Bai Taba Son Ya Zama Shugaban Kasa Ba —Turai

Next Post

‘Yansanda Sun Damke Wani Mutum Da Ya Kashe Matarsa A Adamawa

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

1 week ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

1 week ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

1 week ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

2 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

2 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

2 weeks ago
Next Post
‘Yansanda Sun Damke Wani Mutum Da Ya Kashe Matarsa A Adamawa

'Yansanda Sun Damke Wani Mutum Da Ya Kashe Matarsa A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.